• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

by Abubakar Abba
3 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar bunkasa kiwo ta hanyar cibiyar gudanar da bincken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NAPRI) da ke garin Shika, a Qaramar Hukumar Zaria a Jihar Kaduna, ta gabatar wasu nau’ika takwas na ciyar da Shanu da aka yi wa rijista, bayan aminta da su a shekaru 48 kan daukin da aka samar.

Wannan na kunshe ne, cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar, inda ta bayyana cewa; yin rijistar da kuma fitar da wadannan nau’ika takwas na ciyarwar ciyar da Shanu, wata babbar nasara ce ga ma’aikatar, musamman ganin cewa; ita ce ta farko bayan shekaru 48.

  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Sanarwar ta ce, nau’ikan ciyawar, an mika su ga kwamiti na kasa da ke lura da nau’ikan ciyawa, domin yi wa nau’ikan rijista, sannan kuma a fitar da su.

A cewar sanarwar, nau’ikan ciyawar takwas, sun cimma  matakin amincewa na cibiyar kula da jinsin ciyawa ta kasa, wato GRB da ke garin Ibadan, inda aka gabatarwa da cibiyar domin ta yi musu rijista a kuma fitar da nau’in ciyawar.

“Hakan ya kawo jimlar nau’ika guda dari na ciyawar da aka yi wa rijista a kasar, aka kuma fitar da su, musamman domin a kara bunkasa kiwon Shanu a kasar“, in ji Sanarwar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Sanarwar ta ci gaba da cewa; yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma fitar da su, wani sabon sauyi ne kan samar da ciyawar ciyar da Shanun ciki, har da tsarin samar da ingantaccen Irin noma da kuma kara habaka bangaren kiwon dabbobi a kasar.

A cewar sanawar, hakan kuma zai kara taimakawa a bangaren zuba hannun jarin samar da abincin dabbobi da kara bunkasa kasuwancin abincin dabbobi da kuma kara fitar da abincin nasu, zuwa kasar waje.

Kazalika, ma’aiktar ta bayyana cewa, yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma amincewa da su, hakan zai taimaka wajen tabbatar da kara samar da ingantaccen Irin noma tsaftatacce wanda kuma hakan zai taimaka wa manoman kasar da masu kiwon dabbobi da kuma samar da kyakkyawan yanayi.

“Ingantaccen Irin noman da aka amince da shi ya kasance mai saurin nuna idan an shuka shi, wanda kuma ke jurewa dukkanin wani nau’ikan cututtukan da ke lalata Irin noma“, a cewar sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, hakan zai kuma kara taimakawa wajen kara samar da lafiyar ciyarwar, musamman wadda za ta taimaka wajen kara habaka kiwon dabbobi a dukkanin fadin wannan kasa.

Sanawar ta bayyana cewa, wannan amincewar da aka yi da Irin na noma, ya kai matsayin da ake bukata a hukumance, musamman domin tabbatar da an samar da zabin nau’ikan Irin noman da ake bukata.

A cewar sanarwar, hakan zai kuma taimaka matuka wajen kaucewa yin asara, sakamakon harbin cututtukan da ke kara habaka kasuwa da kara bunkasa zuba hannun jari da kare muhalli da sauran makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaShahu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Next Post

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

6 hours ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

7 hours ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 week ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 week ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

LABARAI MASU NASABA

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.