ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

by Abubakar Abba
1 year ago
Shanu

Ma’aikatar bunkasa kiwo ta hanyar cibiyar gudanar da bincken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NAPRI) da ke garin Shika, a Qaramar Hukumar Zaria a Jihar Kaduna, ta gabatar wasu nau’ika takwas na ciyar da Shanu da aka yi wa rijista, bayan aminta da su a shekaru 48 kan daukin da aka samar.

Wannan na kunshe ne, cikin sanarwar da ma’aikatar ta fitar, inda ta bayyana cewa; yin rijistar da kuma fitar da wadannan nau’ika takwas na ciyarwar ciyar da Shanu, wata babbar nasara ce ga ma’aikatar, musamman ganin cewa; ita ce ta farko bayan shekaru 48.

  • Tsawa Ta Kashe Makiyayi Da Shanu A Kudancin Kaduna
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Sanarwar ta ce, nau’ikan ciyawar, an mika su ga kwamiti na kasa da ke lura da nau’ikan ciyawa, domin yi wa nau’ikan rijista, sannan kuma a fitar da su.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, nau’ikan ciyawar takwas, sun cimma  matakin amincewa na cibiyar kula da jinsin ciyawa ta kasa, wato GRB da ke garin Ibadan, inda aka gabatarwa da cibiyar domin ta yi musu rijista a kuma fitar da nau’in ciyawar.

“Hakan ya kawo jimlar nau’ika guda dari na ciyawar da aka yi wa rijista a kasar, aka kuma fitar da su, musamman domin a kara bunkasa kiwon Shanu a kasar“, in ji Sanarwar.

LABARAI MASU NASABA

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

Sanarwar ta ci gaba da cewa; yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma fitar da su, wani sabon sauyi ne kan samar da ciyawar ciyar da Shanun ciki, har da tsarin samar da ingantaccen Irin noma da kuma kara habaka bangaren kiwon dabbobi a kasar.

A cewar sanawar, hakan kuma zai kara taimakawa a bangaren zuba hannun jarin samar da abincin dabbobi da kara bunkasa kasuwancin abincin dabbobi da kuma kara fitar da abincin nasu, zuwa kasar waje.

Kazalika, ma’aiktar ta bayyana cewa, yi wa nau’ikan ciyawar takwas rijista da kuma amincewa da su, hakan zai taimaka wajen tabbatar da kara samar da ingantaccen Irin noma tsaftatacce wanda kuma hakan zai taimaka wa manoman kasar da masu kiwon dabbobi da kuma samar da kyakkyawan yanayi.

“Ingantaccen Irin noman da aka amince da shi ya kasance mai saurin nuna idan an shuka shi, wanda kuma ke jurewa dukkanin wani nau’ikan cututtukan da ke lalata Irin noma“, a cewar sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, hakan zai kuma kara taimakawa wajen kara samar da lafiyar ciyarwar, musamman wadda za ta taimaka wajen kara habaka kiwon dabbobi a dukkanin fadin wannan kasa.

Sanawar ta bayyana cewa, wannan amincewar da aka yi da Irin na noma, ya kai matsayin da ake bukata a hukumance, musamman domin tabbatar da an samar da zabin nau’ikan Irin noman da ake bukata.

A cewar sanarwar, hakan zai kuma taimaka matuka wajen kaucewa yin asara, sakamakon harbin cututtukan da ke kara habaka kasuwa da kara bunkasa zuba hannun jari da kare muhalli da sauran makamantansu.

Shanu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

MASU ALAKA

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
Shanu
Noma Da Kiwo

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Next Post
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.