ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

by Abubakar Abba
11 months ago
Cocoa

Akwai yiwuwar Nijeriya ta gaza samun damar fitar da Cocoa da ake nomawa a kasar zuwa kasuwannin Tarayyar Turai (EU).

Hakan ka iya faruwa ne, idan har kasar ta gaza cimma ka’idar da EUDR ta gindaya mata daga nan zuwa watan Disambar 2025.

  • Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
  • Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Nijeriya dai, ta kasance ta hudu a duniya wajen nomansa; kana kuma, wadda take kan gaba wajen fitar da shi zuwa kasuwar duniya.

ADVERTISEMENT

Akalla duk shekara, kananan manoma a kasar sun doshi 300,000 tare da noma tan 320,000, inda kuma fannin ke samar da riba; wadda ta kai kimanin dala miliyan 700.

Idan har Nijeriya ta gaza cimma wannan ka’ida ta EUDR, hakan zai iya jawo wa fannin gazawar fitar da shi zuwa Tarayyar Turai (EU).

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

An dai tsara ka’idar ta EUDR ne, domin a yi yaki da illolin muhalli da kuma sare itatuwa.

Yunkurin na daya daga cikin babban aikin yarjejeniyar EU, wadda kuma ta yi daidai da ka’idar ta Tarayyar Turan, musamman domin samar da dabarun bai wa Dazuka kariyar da ta kamata a daukacin fadin duniya baki-daya.

Kazalika, burin da EU ke son cimma shi ne, magance matsalar da Dazuka ke fuskanta tare kuma da tabbatar da ana bin diddigi wajen noman na Cocoa.

Majalisar Tarayyar Turai ta bayyana cewa, ta amince da ka’idar ta EUDR a 2022, wadda kuma ta fara aiki a ranar 29 ga watan Yunin 2023.

Sai dai, ka’idar ta fara aiki ne a ranar 30 ga watan Disambar 2024, wadda kuma cibiyoyin na EU suka daga wa’adin fara aikin ka’idar zuwa ranar 30 ga watan Disambar 2025.

Har ila yau, ka’idar ta bukaci daukacin Cocoa da ake nomawa da kuma jerin sauran amfanin gona, su zamo suna samun kariya tare kuma da tabbatar da an noma su bisa ka’ida.

Su ma kananan sana’oin hannu da matsakaitan sana’oi, akwai wa’adin da aka gindaya musu na su tabbatar da sun kai kayansu, wadanda aka taskance musu zuwa watan Yunin 2026, musamman domin su tabbaar da sun samar da ingantattun kaya.

Duba da cewa, kwana hudu ne kacal suka rage, gwamnatin tarayya ta umarci hukumominta da su tabbatar da sun tsara komai bisa ka’ida, domin kada a ki amincewa da Cocoa da za a fitar da shi zuwa kasuwannin Tarayyar Turan, musamman saboda yadda wasu manoma ke zuba masa sinadaran da ke wuci kima.

Bugu da kari, a ranar Litinin da ta gabata, gwamnatin ta yunkuro wajen karfafa matakan da suka dace na masana’ar Cocoa, domin dakile saba ka’idojin yin nomansa a kasar.

An gudanar da taron tattaunawa na kara jan hankali kan karfafa ka’idar ta EUDR ne a tsakanin Nijeriya da EU, a fadar shugaban kasa da ke Abuja, musamman domin a tabbatar da Nijeriya ta cimma wa’adin ranar da aka gindaya mata.

Dakta Kingsley Uzoma, Babban Mai Taimka Wa Shugaban Kasa a bangaren noma, domin samun riba da habaka fannin noma a jawabinsa a wajen tattaunawar ya sanar da cewa, Nijeriya a shirye take wajen cika ka’idar ta EUDR.

Uzoma ya bayyana cewa, manufar tattaunawar a kan batun ka’dar ta EUDR, wadda kuma ta haramta barin fitar da Cocoa da sauran amfanin gona da suke da illa zuwa kasuwar ta EU.

Ya ci gaba da cewa, fannin na noman Cocoa wani babban ginshike ne da ke kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

Daga 2023 zuwa 2024, Afirka ta noma Cocoa da ya kai kimanin tan miliyan 3.151, inda Nijeriya ta noma tan 320,000 tare da kuma bukatar kara fadada nomansa zuwa tan 500,000 a 2025, ta hanyar shirye-shiryen da ta kirkiro da su.

Bisa wasu alkaluman da Hukumar Kididdga ta Kasa (NBS) ta fitar sun nuna cewa; a zango na karshe na 2024, Nijeriya ta fitar da karin Cocoa da ya kai kimanin kashi 606, wanda ya kai na kusan Naira biliyan 171 a zango na karshe na 2023 zuwa Naira biliyan 1.2.

Cocoa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.