• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru 9 a jere ke nan, WHA, watau dandalin koli na tattaunawa na hukumar lafiya ta duniya (WHO) na kin amincewa da bukatar yankin Taiwan na halartar taronsa. 

Idan yankin Taiwan da masu zuga shi ba za su gaji da neman ta da hargitsi ba, to ba za mu gaji da jaddada musu cewa, yunkurinsu na ballewa ba zai taba cimma nasara ba, kuma yankin zai ci gaba da kasancewa wani bangare na kasar Sin da ba zai iya ballewa ba.

  • Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo
  • Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

Manufar kasancewar Sin daya tak kuma halaltacciya mai wakiltar dukkan yankunan kasar, abu ne da daukacin kasashen duniya suka amince da shi, haka kuma kuduri ne mai lamba 2758 da MDD ta zartas, da ya kamata kasa da kasa su yi biyayya gare shi.

Idan Taiwan na ganin tana samun goyon baya daga wata kasa mai karfi, to kasashe 183 a duniya ne suka riga suka kulla huldar diplomasiyya da Sin bisa amincewa da manufar kasar Sin daya tak a duniya, don haka, sarkin yawa ya fi sarkin karfi.

Kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa a duniya ta kowacce fuska, ciki har da tallafi da hadin gwiwa a bangaren lafiya da kasa da kasa, inda ta shafe shekaru sama da 60 tana tura jami’an lafiya da kwararru zuwa kasashen dake fadin duniya. Don haka tabbas Sin tana da iko, kuma ita ta cancanta ta kula da duk wasu harkoki na Taiwan ba wai yankin ya yi gaban kansa wajen nuna shi ’yantacce ne ba. Baya ga haka, kasar Sin tana ba yankin damarmaki ana damawa da shi a harkokin hukumar ta WHO da ma ba shi damar samun bayanai da rahotanni na gaggawa daga hukumar, karkashin manufarta ta “kasa daya mai tsarin mulki 2”. Bugu da kari, kasar Sin ta kasance mai sanya muradun al’ummarta gaba da komai, don haka, ba ta taba barin mutanenta na yankin a baya ba.

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

A bana ake cika shekaru 80 da kawo karshen yakin duniya na II da ma dawowar yankin Taiwan karkashin ikon babban yankin kasar Sin, wadda nasara ce da babu wanda zai goyi bayan lalata ta, sai masu neman cimma wani buri na kansu. La’akari da shekarun da aka shafe, da tsayawar kasar Sin tsayin daka kan tabbatar da iko kan yankunanta, ya kamata yankin Taiwan da masu tunzura shi su fahimci cewa, suna bata lokacinsu domin manufar kasar Sin daya tak, manufa ce da ta samu amincewar kasa da kasa kuma babu wanda zai iya sauyata. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo

Next Post

An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

11 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

12 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

13 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

14 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

15 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

16 hours ago
Next Post
An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka

An Tattauna Hanyar Zamanantar Da Kasa A Dandalin Tattaunawa Na Masanan Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.