• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

by Khalid Idris Doya
11 hours ago
in Labarai
0
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kamfanin Man Fetur na kasa NNPCL, Bayo Ojulari, ya sanar da shirye-shiryen dawo da ayyukan ci gaba da neman Man a Kolmani, da ke a yankin Arewa maso Gas.

Idan za a iya tunawa, a ranar 22 na watan Nuwambar 2022 ne, tsohuwar Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ta kaddamar da aikin hako Man na Kolmani, wanda aikin ya kasance, shi ne na farko da aka fara gudnarwa a Arewacin kasar.

  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Ojulari wanda ya sanar da hakan a hirarsa da kafar BBC a ranar Litinin ya yi kira ga alumomin da ke a yankin na Arewa maso Gabas da su kawantar da hankulansu tare da ba su tabbacin cewa, za a sake dawo da aikin na neman Man a Kolmani da ke a yankin Arewa maso Gabas.

“Zamu dawo da aikin na neman Man a Kolmani da kuma a sauran guraren da ake hasashen akwai Man Fetur din, baya ga batun neman Man, mun kuma mayar da hankali wajen kammala aikin sanya Bututun Danye daga Ajaokuta zuwa jihar Kano,” Inji Ojulari.

Ya sanar da cewa, wadannan ayyukan, za su taimaka wajen sake dawo da masana’antu da durkushe da kuma sake kafa wasu sabbin masana’antu.

Labarai Masu Nasaba

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

“Wannan ci gaban zai kuma taimaka wajen kara habaka tattalin ardikin da ke a yankin na Arewa maso Gabas, wanda hakan ya zame mana wajbi, mu sake dawo wajen yin aikin domin aikin ya ci gaba da tafiya,” A cewar Ojulari.

Kan batun rikicin da yaki ci, yaki cinyewa a tsakanin Kamfanin na NNPCL da kuma rukunomin Kamfanin Dangote Ojulari ya bayyana cewa, ana ci gaba da kokari domin a kawo karshen rikicin.

“Dangote ya bayar da gagarumar gudunmawa wanda kuma, ya cannaci a yaba masa, za mu kuma yi hadaka domin mu tabbatar da, mun ci gaba da samar da wadataccen Man Fetur ga ‘yan kasar nan,” Inji Sabon Shugaban.

“Ana samun masalaha kan komai ne, ta hanyar tattaunawa za mu yi aiki kafada da kafada, domin amfanin ‘yan Nijeriya,” A cewar Ojulari.

Kazalika, da yake yin tsokaci kan batun samun raguwar farashin Danyen Mai a kasuwar duniya wanda hakan ya sanya burin samun kudaden shiga na kasar ya ragu, ya sanar da cewa, hakan ya shafi kasafin kudin kasar, duba da cewa, akasarin hasashen kasar ya dogara ne, kan samun kudin shiga na Man.

Ya sanar da cewa, NNPCL na kan aikin rage kashe kudaden gudanar da ayyukansa, wanda hakan zai bai wa Kamfanin damar yin amfani da kudaden shigar da yake samu, ta hanyar sayar da Man Fetur da na Iskar Gas.

Kan korafin da wasu yan kasar ke yi, kan rashin raguwar farashin Man Fetur da ake sayarwa a kasar, duk da cewa, farashinsa ya ragu a kasuwar duniya ya ce, Dilolin Man na bukatar lokaci, domin rage farashinsa.

“Idan Dilalan sun sayi Man kafin farashinsa ya ragu, suna bukatar su sayar da shi ne, kan tsohon farashi, amma idan sun saye shi kasa da sabon farashi, muna sa ran farashin ya sauka wanda zai nuna cewa, an samu sauyi,” Inji Ojulari.

A cewar NNPCL, tarin aikin na neman Man na Kolmani, an faro shi ne, tare da Kamfanin Mai na Shell a 1970, amma daga baya, aka yi watsi da aikin domin ba samu wata gagarumar cimma nasara ba.

Sai dai, daga baya an sake dawo da aikin ta hanyar Kolmani Riber 2, 3, and 4 a shekarar 2019, wanda hakan ya sanya aka gano Gangunan Danyen Mai biliyan daya da kuma Iskar Gas biliyan 500.

NNPC a ya sanar da cewa, a 2019 ya sake gabata da bukatar a yi amfani da kimiyyar zamani domin a ci gaba da aikin na nemna Man Kolmani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NNPCL
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci Kada Amurka Ta Siyasantar Da Hadin Gwiwar Bangaren Ilimi

Next Post

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Related

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

3 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

5 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

8 hours ago
Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3
Ilimi

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

21 hours ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

23 hours ago
Next Post
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

May 24, 2025
Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon Ɗan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

Mohamed Salah Ya Zama Gwarzon Ɗan Wasan Firimiyar Ingila Na Bana

May 24, 2025
Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara

Yadda Za Ki Hada Garin Sakwara

May 24, 2025
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

May 24, 2025
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

May 24, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata

May 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.