• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar Jihar Yobe sun na ci gaba da alhinin kisan gillar da aka yi wa Shehin Malamin addinin Musulunci, Sheikh Goni Aisami Gashuwa, wanda ake zargin wasu jami’an tsaro ne suka kashe shi.

Ana zargin sun kashe shi da misalin karfe 10:00 na daren ranar Juma’a, kan hanyarsa ta dawowa daga Kano zuwa Gashuwa.

  • Yanzu-Yanzu: SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Ganawa Da Ministan Ilimi
  • Babu Wanda Zai Fice Daga NNPP Da Zai Girgiza Siyasar Kwankwaso – Kofa

Kamar yadda wata majiya daga bakin wani jami’in tsaro a garin Jaji-maji, shelkwatar karamar hukumar Karasuwa ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, maharan sun biyo shi ne a mota kirar Sharon, wanda suka tare motarsa bayan ya fita daga kauyen Chakama mai tazarar kilomita 3 zuwa garin Jaji-maji.

“Shi kadai ne a motar kuma da alama sun biyo shi ne ne bisa zaton yana dauke da kudi, a kan hanyarsa daga Kano zuwa gida. Wanda bayan sun harbe shi a ciki tare da soka masa wuka a jiki, sannan suka ja gawarsa zuwa gindin kaba. Kuma cikin ikon Allah basu bar inda gawarsa take ba har gari ya waye.”

“Ana haka sai ga jama’a masu tafiya gona, wanda nan take suka shaida wa Lawanin Jaji-maji, Lawan Manaja inda nan take ya nemi ‘yansanda da ke aiki a garin.” In ji majiyar.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Bugu da kari, majiyar tsaro a garin Jaji-maji ta bayyana cewa, “Ana zargin wasu sojoji biyu da kisan malamin, wanda kuma tuni ‘yansanda suka kama su tare da bindigogi biyu.

“Sannan zancen da nake da kai yanzu haka an garzaya dasu zuwa Damaturu, babban birnin Jihar Yobe don ci gaba da bincike,” a cewarsa.

A hannu guda kuma, wannan rashi na Sheikh Goni Aisami Gashuwa, ya tayar da hankulan al’ummar garin Gashuwa da Jihar Yobe baki daya, saboda kasancewarsa mutum mai kokari kuma Malami mai karantar da al’umma sama da shekaru 30 da suka gabata.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim, ya tabbatar wa da wakilinmu a jihar cewa, sun samu bayanin afkuwar lamarin tare da kokarin da jami’ansu a garin suka yi na kama wadanda ake zargi da aikata laifi.

Ya kara da cewa yanzu haka suka hannun jami’an tsaron binciken manyan laifuka (CID) a Damaturu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAlhiniJami'an TsaroKisan gillaSheikh Goni GashuwaYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-Yanzu: SSANU Da NASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Ganawa Da Ministan Ilimi

Next Post

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

13 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

22 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

24 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.