Ƙungiyar League of Northern Democrats (LND) ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau, ta bayyana cewa sai an kafa sabuwar jam’iyyar siyasa ne za ta shiga cikin haɗakar ‘yan adawa da ke shirin korar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu daga mulki a zaɓen 2027.
Shugaban ƙungiyar, Dr. Umar Arɗo, tare da wasu manyan mambobi 12, sun bayyana hakan cikin wata sanarwa da suka fitar a ranar Lahadi, inda suka ce sun duba zaɓi biyu da ake da su — shiga cikin jam’iyyar ADC ko SDP, ko kuma kafa sabuwar jam’iyya daga tushe.
- ‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
- Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
Sanarwar ta nuna cewa duk da ana raɗe-raɗin cewa haɗakar ‘yan adawa ƙarƙashin jagorancin Atiku Abubakar da tsoffin gwamnoni irin su Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi za su yi amfani da wata tsohuwar jam’iyya, amma ƙungiyar LND na ganin hakan zai iya jawo rikice-rikice da rikicin shugabanci.
Arɗo ya bayyana cewa, “Jam’iyyun da ke akwai irin su ADC da SDP suna da tsarin shugabanci da aka kafa bisa doka wanda sau da yawa ba ya karɓar sauyi. Misali, shugaban ADC a Adamawa ya ce wa’adinsa yana nan daram har zuwa Disamba 2026. Wannan yanayi ne da ke akwai a sassa daban-daban na ƙasa.”
A cewarsa, kafa sabuwar jam’iyya zai bayar damar samar da sabon tunani da tsari, da kuma sabunta siyasa wanda zai iya karɓuwa a zuƙatan ‘yan Nijeriya da suka gaji da tsoffin jam’iyyu da alƙawarin da ba a cika ba.
Ya buƙaci shugabannin haɗakar su fara tsarin kafa sabuwar jam’iyyar da za ta kasance mai suna ɗaya, falsafa ɗaya, da tsarin shugabancin da zai haɗa kan kowa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp