ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Shekarau

Ƙungiyar League of Northern Democrats (LND) ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Jihar Kano, Ibrahim Shekarau, ta bayyana cewa sai an kafa sabuwar jam’iyyar siyasa ne za ta shiga cikin haɗakar ‘yan adawa da ke shirin korar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu daga mulki a zaɓen 2027.

Shugaban ƙungiyar, Dr. Umar Arɗo, tare da wasu manyan mambobi 12, sun bayyana hakan cikin wata sanarwa da suka fitar a ranar Lahadi, inda suka ce sun duba zaɓi biyu da ake da su — shiga cikin jam’iyyar ADC ko SDP, ko kuma kafa sabuwar jam’iyya daga tushe.

  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
  • Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Sanarwar ta nuna cewa duk da ana raɗe-raɗin cewa haɗakar ‘yan adawa ƙarƙashin jagorancin Atiku Abubakar da tsoffin gwamnoni irin su Nasir El-Rufai da Rotimi Amaechi za su yi amfani da wata tsohuwar jam’iyya, amma ƙungiyar LND na ganin hakan zai iya jawo rikice-rikice da rikicin shugabanci.

ADVERTISEMENT

Arɗo ya bayyana cewa, “Jam’iyyun da ke akwai irin su ADC da SDP suna da tsarin shugabanci da aka kafa bisa doka wanda sau da yawa ba ya karɓar sauyi. Misali, shugaban ADC a Adamawa ya ce wa’adinsa yana nan daram har zuwa Disamba 2026. Wannan yanayi ne da ke akwai a sassa daban-daban na ƙasa.”

A cewarsa, kafa sabuwar jam’iyya zai bayar damar samar da sabon tunani da tsari, da kuma sabunta siyasa wanda zai iya karɓuwa a zuƙatan ‘yan Nijeriya da suka gaji da tsoffin jam’iyyu da alƙawarin da ba a cika ba.

LABARAI MASU NASABA

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Ya buƙaci shugabannin haɗakar su fara tsarin kafa sabuwar jam’iyyar da za ta kasance mai suna ɗaya, falsafa ɗaya, da tsarin shugabancin da zai haɗa kan kowa.

Shekarau
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
  • Abubakar Sulaiman
    Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

MASU ALAKA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Labarai

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Next Post
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
Shekarau

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.