• English
  • Business News
Sunday, September 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
4 months ago
in Wasanni
0
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Inter Milan da kocinta Simone Inzaghi sun raba gari ta hanyar yarjejeniya, kwanaki uku bayan da Paris St-Germain (PSG) ta doke su a gasar cin kofin zakarun Turai. Inzaghi mai shekaru 49, wanda kulob din Serie A din ya nada a shekarar 2021, yana da alaka mai karfi tsakaninshi da kungiyar Al-Hilal ta kasar Saudiyya.

 

“Lokaci ya yi da zan yi bankwana da wannan kulob bayan aikin shekaru hudu, inda na ba da komai domin samun nasararta,” in ji Inzaghi wanda ya lashe kofuna shida a Inter.

  • ‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah
  • Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A FaÉ—in Ƙasa Baki ÆŠaya

“Ina so in furta kalma daya ta karshe ga miliyoyin magoya bayan Nerazzurri (Inter) wadanda suka taya ni murna a lokacin nasara, hakazalika suka taya ni kuka a lokuta masu wahala kuma suka yi dariya da murna a kofuna shida da muka samu tare”.

 

Labarai Masu Nasaba

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Sanarwar tafiyar tasa ta biyo bayan ganawar da Inzaghi ya yi da jami’an Inter a ranar Talata, sanarwar da Inter Milan ta fitar ta ce Kulob din da Simone Inzaghi sun yanke shawarar rabuwa, “Wannan shi ne shawarar da aka dauka bisa yarjejeniyar juna”, shugaban Inter Giuseppe Marotta ya kara da cewa “Ina so in gode wa Simone Inzaghi saboda aikin da ya yi, ya matukar taka rawar gani a shekaru 4 da muka shafe muna aiki tare, don haka Inter Milan na yi mashi fatan alheri a duk inda zai samu kanshi a nan gaba”.

 

Inzaghi ya lashe gasar Seria A daya, Coppa Italia biyu da kuma Supercoppa Italia sau uku a lokacin da ya ke San Siro, sau biyu ya jagoranci Inter zuwa wasan karshe na gasar zakarun Turai amma Manchester City ta doke su da ci 1-0 a 2022-23 sannan suka sha kashi a hannun PSG da ci 5-0 a ranar Asabar din da ta gabata.

 

Sun kuma kasa cin kofin Seria A na 2024-25 bayan da Napoli ta basu maki daya kacal akan teburi, tafiyar Inzaghi na zuwa ne gabanin halartar Inter a gasar cin kofin duniya na kungiyoyin kwallon kafa na Fifa da aka fadada, wanda zai gudana a Amurka tsakanin 14 ga watan Yuni zuwa 13 ga Yuli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Next Post

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Related

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano
Wasanni

Atletico Madrid Ta Zazzaga Wa Real Madrid Ƙwallaye 5 A Metropolitano

15 hours ago
Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5
Wasanni

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

3 days ago
An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
Wasanni

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

4 days ago
Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata
Wasanni

Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

4 days ago
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
Manyan Labarai

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

5 days ago
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
Manyan Labarai

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

5 days ago
Next Post
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

September 28, 2025
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

September 28, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira

September 27, 2025
Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

September 27, 2025
Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

September 27, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

September 27, 2025
Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

September 27, 2025
Yadda Ake Hada Sushi

Yadda Ake Hada Sushi

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.