ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Al’ummar yankin Latin Amurka sun shiga wannan mako da kafar dama, biyo bayan manufar gwajin da kasar Sin ta fara aiwatarwa a ranar Lahadin da ta gabata, na ba ’yan kasashen Brazil da Argentina da Chile da Peru da ma Uruguay, damar shigowa kasar ba tare da biza ba har na tsawon kwanaki 30, domin gudanar da harkokin da suka shafi kasuwanci da ziyara da bude ido da yada zango ko kuma harkokin da suka shafi al’adu. 

Babu makawa, duk abun da kasar Sin ta furta, to da gaske take. Kuma duk burin da ta sanya a gaba, za ta dage wajen kai wa ga cimma masa. Cikin rahoton aikin gwamnati da aka fitar yayin manyan taruka biyu da aka yi a watan Maris na bana, gwamnatin kasar Sin ta nanata niyyarta ta fadada bude kofa, tana cewa ba tare da la’akari da duk wani sauyi da duniya za ta tsinci kanta ciki ba, Sin za ta ci gaba da bude kofarta ga kasashen waje. Wannan ya nuna muradin kasar Sin na ganin kasashen duniya sun samu ci gaba na bai daya da inganta huldar tsakanin sassan duniya da ma goyon bayanta ga dunkulewar tattalin arzikin duniya.

  • Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
  • Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

A yanayin da aka shiga a duniya, babu wata kasa ko al’umma da za ta kebe kanta ita kadai ko rufe kofarta, sannan ta yi tsammanin samun ci gaba ko fifiko kan sauran kasashe. Kulle kofa da wasu kasashe ke son yi, ba zai kai ga muradin da ake son cimmawa na tabbatar da zaman lafiya da habakar tattalin arzikin duniya ba. Mun gani a baya-bayan nan, yadda harkokin cinikayya da tsarin samar da kayayyaki suka hargitse biyo bayan ra’ayin kariya da neman iko.

ADVERTISEMENT

Galibin matsalolin da ake samu tsakanin kasa da kasa da al’ummomin duniya, ya samo asali ne daga rashin fahimta ko yaduwar karairayi, amma cudanyar kasa da kasa da al’ummominsu ta hanyar bude kofa da maraba da juna, zai kara ba da damar fahimta da warware gaskiya da karya, ta yadda za a kai ga inganta fahimtar juna. Wannan na nuna cewa, bude kofa bai tsaya ga amfanawa bangaren tattalin arziki da cinikayya ba kadai, ya kai ga daukaka zaman lafiya da kyautata zamantakewa da samun ci gaba da samar da aikin yi da wayewar kai da kirkire-kirkire da sauransu.

Zuwa yanzu, matakin Sin game da bizar a bana, bai tsaya kan kasashen Latin Amurka ba, su ma ’yan kasashen Saudiyya da Oman da Kuwait da Bahrain, za su more wannan dama daga ranar 9 ga watan nan, har zuwa 8 ga watan Yunin 2026. Haka kuma, an fadada tsarin yada zango na tsawon sa’o’i 240 ga matafiya daga kasashe 54 ba tare da biza ba.

LABARAI MASU NASABA

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Irin manufar bude kofa da gyare-gyare ta kasar Sin duniya da jama’arta suka fi bukata, domin ita ce za ta bada damar samun dunkulewar duniya da ci gabanta kamar yadda ake fata, har ma da kai wa gina duniya mai kyakkyawar makoma ga dukkannin dan adam. (Fa’iza Mustapha)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Taya Andy Burnham Murnar Zama Sabon Firaministan Birtaniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Gabatar Da Matakan Bunkasa Bangaren Bayar Da Hidimomi A Cikin Gida
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Bayar Da Tallafin Sama Da Ton 3,000 Na Abinci Ga Sudan Ta Kudu
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah
  • Sulaiman
    An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”
  • Sulaiman
    Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
  • Sulaiman
    Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

MASU ALAKA

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nuna Matukar Rashin Amincewarta Ga Jakadan Philippines Kan Tsokanar Fada A Ren’ai Jiao

July 21, 2026
Next Post
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

LABARAI MASU NASABA

Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.