• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Dogara

Tsohon Kakakin Majalisar wakilai ta tarayya, Rt. Hon. Yakubu Dogara ya aike da wasikar korafi wa Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya, IGP Usman Baba Alkali dangane da zargin yunkurin kasheshi da wani dan mazabarsa ke yi.

Tsohon Kakakin ya bayyana sunansa wanda ke kokarin kashe sa din da cewa shine Barau Joel Amos wanda a cewarsa balo-balo ya yi ikirarin zai sayi bindiga tare da kashe shi da wasu ‘yan mazabarsa su uku masu suna Barr. Istifanus Bala Gambar, Rabaran Markus Musa (Shugaban kungiyar Kiristoci na Tafawa Balewa) da Mr. Emmanuel (Shugaban NL, na T/Balewa).

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

Yakubu Dogara ya shaida wa IGP Alkali cewa akwai zargin hada kai da wasu jami’an ‘yansanda masu suna Insifekta Dakat Samuel da Insifekta Auwalu Mohammed da shi Barau Joel Amos (Sarkin Yaki) wajen shirya wannan makarkashiyar tare da sayen bindigogi a hannunsu domin kashe shi.

Dogara ya shaida wa shugaban ‘yansandan cewa tunin kes din yake gaban DCP na sashin binciken na manyan laifuka ta rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, amma bisa girman lamarin ya ga dacewar sanar da shi domin fadada bincike, “Batu ne da ya shafi sace makamanku daga wasu jami’an da aka daura wa alhakin kula da makamai a wurin adanasu, shi Barau Joel Amos ko zai saya ko yana ma yana sayen bindigogi daga wajen jami’an.”

Dogara ya kara da cewa abun mamakin shine babu wani shawara a hukumance da ‘yansanda suka fitar dangane da wannan mummunar barazanar da ake yi wa rayuwarsu duk kuwa da cewa ana samun kesa-kesan garkuwa da mutane da kashe wasu ma musamman a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Dogaran sai ya buga misali da harin baya-bayan nan da wasu ‘yan bindiga suka kai kauyen Boto da ke gundumar Lere inda suka yi garkuwa da ‘yan uwan tsohon gwamnan Jihar Bauchi, Ahmadu Adamu Mu’azu da kashe wani, kan hakan ya nuna cewa akwai bukatar daukan matakan kan lamarin.

Ya ce irin wannan lamarin abun ne da ke bukatar gaggauta daukar matakin tare da cafke Barau Joel Amos domin zufafa bincike.

Hon. Yakubu Dogara ya kuma ce akwai matukar bukatar a binciki Barau Amos kan matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin tare da bincikar inda yake samun kudaden sayen makamai tare da bibiyar bayanan shigar kudi da fitar kudi na asusun ajiyarsa hadi da binciken wayarsa.

Ya ce akwai bayanan da suke da su da dama da ke nuna cewa shi Barau Joel Amos na da hannu a zarge-zarge da dama don haka akwai bukatar a tsare shi tare da zurfafa bincike a kansa.

Ya yi fatan cewa Shugaban na ‘yansanda ba zai yi wasa da wannan batun ba inda zai kaddamar da bincike domin tabbatar da inganci tsaro da kare rayuka da dukiyar jama’an yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Next Post
Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.