ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Jami'an Tsaro

Akalla mutane 69 ne aka samu nasarar ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane a jihar Bauchi sakamakon aikin hadin guiwa tsakanin jami’an tsaro da kungiyoyin sa-kai irin su ‘yan Bijilante da ‘yan Nanga wadanda suka kutsa kai maboyar masu garkuwan a cikin dazuka tare da ceto mutanen.

Wannan bayanin ya fito daga bakin kwamishinan kananan hukumomi da kula da Masarautun gargajiya na jihar Bauchi, Hon. Abdulrazaq Nuhu Zaki yayin da ke ganawa da ‘yan jarida a jiya.

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 32 Daga Masu Garkuwa
  • Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Ya ce, tun lokacin da aka fara samun ‘yan matsalolin tsaro a jihar gwamnati da sarakuna hadi da jami’an tsaro tare da shugabannin kananan hukumomi suka bazama kokarin dakile aniyar bata-garin inda suka cimma muhimman nasarori kan hakan.

ADVERTISEMENT

Ya ce, jami’an tsaron sun yi ta sintiri zuwa dazukan da ‘yan ta’addan ke fakewa inda suka fatattaki wasu tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su da dama.

A kan hakan ya ce yanzu jihar Bauchi ta samu kwanciyar hankali daga barazanar masu garkuwa da mutane, “Domin koda wasa gwamna Bala Muhammad baya sakaci da harkokin da suka shafi tsaro. Lamari na tsaro na faruwa zai tashi tsaye.”

LABARAI MASU NASABA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

A cewarsa an samu kwararowar ‘yan garkuwa da mutane cikin dazuka a Toro, Alkaleri, Tafawa Balewa da karamar hukumar Ningi wanda kuma tunin hukumomi suka yi abubuwan da suka dace domin dakile yunkurin su. Yana mai cewa wasu ma ba ‘yan jihar Bauchi ba ne.

A cewarsa: “Gwamna Bala Muhammad da kansa yake jagorantar yaki da wannan matsalar. Ya sha ziyartar yankunan da matsalar ya shafa tare da jajanta musu da kuma karfafa musu guiwar su dake su jajirce wajen tunkarar masu garkuwan daidai da karfinsu. Hakan ya kara wa jama’a kumaji da farkawa.

“Da hadin guiwar shugabannin kananan hukumomin jihar da shi kansa gwamnan Bala Muhammad da jami’an tsaro muna kan magance ‘yan kananan matsalolin tsaro da suke akwai. Domin shi gwamna bai wasa ko kadan a kan hidimar tsaro. Domin shi gwamnan ya karfafi masu ruwa da tsaki kan yin abun da ya dace.

“A wannan fatattakar da aka yi wa ‘yan ta’addan an samu nasarar kwato mutane 69 a sassa daban-daban na jihar Bauchi.”

Nuhu Zaki ya ce tunin gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad ya fara tattaunawa da Gwamnatin jihar Fitato da Taraba da suka iya iyaka da jihar domin ganin an hada kai wajen yin sintirin hadin guiwa domin kawo karshen ‘yan ta’addan da ke buya a cikin dazukan jihohin ukun.

Jami'an Tsaro
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.