ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Jami'an Tsaro

Akalla mutane 69 ne aka samu nasarar ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane a jihar Bauchi sakamakon aikin hadin guiwa tsakanin jami’an tsaro da kungiyoyin sa-kai irin su ‘yan Bijilante da ‘yan Nanga wadanda suka kutsa kai maboyar masu garkuwan a cikin dazuka tare da ceto mutanen.

Wannan bayanin ya fito daga bakin kwamishinan kananan hukumomi da kula da Masarautun gargajiya na jihar Bauchi, Hon. Abdulrazaq Nuhu Zaki yayin da ke ganawa da ‘yan jarida a jiya.

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 32 Daga Masu Garkuwa
  • Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Ya ce, tun lokacin da aka fara samun ‘yan matsalolin tsaro a jihar gwamnati da sarakuna hadi da jami’an tsaro tare da shugabannin kananan hukumomi suka bazama kokarin dakile aniyar bata-garin inda suka cimma muhimman nasarori kan hakan.

ADVERTISEMENT

Ya ce, jami’an tsaron sun yi ta sintiri zuwa dazukan da ‘yan ta’addan ke fakewa inda suka fatattaki wasu tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su da dama.

A kan hakan ya ce yanzu jihar Bauchi ta samu kwanciyar hankali daga barazanar masu garkuwa da mutane, “Domin koda wasa gwamna Bala Muhammad baya sakaci da harkokin da suka shafi tsaro. Lamari na tsaro na faruwa zai tashi tsaye.”

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

A cewarsa an samu kwararowar ‘yan garkuwa da mutane cikin dazuka a Toro, Alkaleri, Tafawa Balewa da karamar hukumar Ningi wanda kuma tunin hukumomi suka yi abubuwan da suka dace domin dakile yunkurin su. Yana mai cewa wasu ma ba ‘yan jihar Bauchi ba ne.

A cewarsa: “Gwamna Bala Muhammad da kansa yake jagorantar yaki da wannan matsalar. Ya sha ziyartar yankunan da matsalar ya shafa tare da jajanta musu da kuma karfafa musu guiwar su dake su jajirce wajen tunkarar masu garkuwan daidai da karfinsu. Hakan ya kara wa jama’a kumaji da farkawa.

“Da hadin guiwar shugabannin kananan hukumomin jihar da shi kansa gwamnan Bala Muhammad da jami’an tsaro muna kan magance ‘yan kananan matsalolin tsaro da suke akwai. Domin shi gwamna bai wasa ko kadan a kan hidimar tsaro. Domin shi gwamnan ya karfafi masu ruwa da tsaki kan yin abun da ya dace.

“A wannan fatattakar da aka yi wa ‘yan ta’addan an samu nasarar kwato mutane 69 a sassa daban-daban na jihar Bauchi.”

Nuhu Zaki ya ce tunin gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad ya fara tattaunawa da Gwamnatin jihar Fitato da Taraba da suka iya iyaka da jihar domin ganin an hada kai wajen yin sintirin hadin guiwa domin kawo karshen ‘yan ta’addan da ke buya a cikin dazukan jihohin ukun.

Jami'an Tsaro
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.