• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Siyasa
0
Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Kakakin Majalisar wakilai ta tarayya, Rt. Hon. Yakubu Dogara ya aike da wasikar korafi wa Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya, IGP Usman Baba Alkali dangane da zargin yunkurin kasheshi da wani dan mazabarsa ke yi.

Tsohon Kakakin ya bayyana sunansa wanda ke kokarin kashe sa din da cewa shine Barau Joel Amos wanda a cewarsa balo-balo ya yi ikirarin zai sayi bindiga tare da kashe shi da wasu ‘yan mazabarsa su uku masu suna Barr. Istifanus Bala Gambar, Rabaran Markus Musa (Shugaban kungiyar Kiristoci na Tafawa Balewa) da Mr. Emmanuel (Shugaban NL, na T/Balewa).

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

Yakubu Dogara ya shaida wa IGP Alkali cewa akwai zargin hada kai da wasu jami’an ‘yansanda masu suna Insifekta Dakat Samuel da Insifekta Auwalu Mohammed da shi Barau Joel Amos (Sarkin Yaki) wajen shirya wannan makarkashiyar tare da sayen bindigogi a hannunsu domin kashe shi.

Dogara ya shaida wa shugaban ‘yansandan cewa tunin kes din yake gaban DCP na sashin binciken na manyan laifuka ta rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, amma bisa girman lamarin ya ga dacewar sanar da shi domin fadada bincike, “Batu ne da ya shafi sace makamanku daga wasu jami’an da aka daura wa alhakin kula da makamai a wurin adanasu, shi Barau Joel Amos ko zai saya ko yana ma yana sayen bindigogi daga wajen jami’an.”

Dogara ya kara da cewa abun mamakin shine babu wani shawara a hukumance da ‘yansanda suka fitar dangane da wannan mummunar barazanar da ake yi wa rayuwarsu duk kuwa da cewa ana samun kesa-kesan garkuwa da mutane da kashe wasu ma musamman a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

Dogaran sai ya buga misali da harin baya-bayan nan da wasu ‘yan bindiga suka kai kauyen Boto da ke gundumar Lere inda suka yi garkuwa da ‘yan uwan tsohon gwamnan Jihar Bauchi, Ahmadu Adamu Mu’azu da kashe wani, kan hakan ya nuna cewa akwai bukatar daukan matakan kan lamarin.

Ya ce irin wannan lamarin abun ne da ke bukatar gaggauta daukar matakin tare da cafke Barau Joel Amos domin zufafa bincike.

Hon. Yakubu Dogara ya kuma ce akwai matukar bukatar a binciki Barau Amos kan matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin tare da bincikar inda yake samun kudaden sayen makamai tare da bibiyar bayanan shigar kudi da fitar kudi na asusun ajiyarsa hadi da binciken wayarsa.

Ya ce akwai bayanan da suke da su da dama da ke nuna cewa shi Barau Joel Amos na da hannu a zarge-zarge da dama don haka akwai bukatar a tsare shi tare da zurfafa bincike a kansa.

Ya yi fatan cewa Shugaban na ‘yansanda ba zai yi wasa da wannan batun ba inda zai kaddamar da bincike domin tabbatar da inganci tsaro da kare rayuka da dukiyar jama’an yankin.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Afirka Zata Iya Lashe Kofin Duniya A Qatar – Samuel Eto’o 

Next Post

Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Related

Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)
Manyan Labarai

PDP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Zaben Kaduna Da Ta Tabbatar Da Nasarar Uba Sani

3 days ago
Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

4 days ago
Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)
Manyan Labarai

Kotun Zabe Ta Ce Zaben Gwamnan Kaduna Bai Kammalu Ba (Inconclusive)

4 days ago
NNPP Ta Yi Watsi Da Hukuncin Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano Da Ta Ba Gawuna Nasara
Siyasa

NNPP Ta Kai Korafinta Ga Hukumar NJC Kan Kalaman Daya Da Cikin Alkalan Kotun Zaben Kano

5 days ago
Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin
Manyan Labarai

Kotun Sauraren Karar Zaben Gwamna A Legas Za Ta Yanke Hukunci Ranar Litinin

1 week ago
Shari’ar Zaben Gwamnan Bauchi: Sai Mun Ga Abin Da Ya Ture Wa Buzu Nadi – Dan Takarar APC
Siyasa

Shari’ar Zaben Gwamnan Bauchi: Sai Mun Ga Abin Da Ya Ture Wa Buzu Nadi – Dan Takarar APC

1 week ago
Next Post
Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.