ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwata Na Cikin Hatsari, Ana Kokarin Kashe Ni – Yakubu Dogara

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Dogara

Tsohon Kakakin Majalisar wakilai ta tarayya, Rt. Hon. Yakubu Dogara ya aike da wasikar korafi wa Sufeto Janar na ‘yansandan Nijeriya, IGP Usman Baba Alkali dangane da zargin yunkurin kasheshi da wani dan mazabarsa ke yi.

Tsohon Kakakin ya bayyana sunansa wanda ke kokarin kashe sa din da cewa shine Barau Joel Amos wanda a cewarsa balo-balo ya yi ikirarin zai sayi bindiga tare da kashe shi da wasu ‘yan mazabarsa su uku masu suna Barr. Istifanus Bala Gambar, Rabaran Markus Musa (Shugaban kungiyar Kiristoci na Tafawa Balewa) da Mr. Emmanuel (Shugaban NL, na T/Balewa).

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

Yakubu Dogara ya shaida wa IGP Alkali cewa akwai zargin hada kai da wasu jami’an ‘yansanda masu suna Insifekta Dakat Samuel da Insifekta Auwalu Mohammed da shi Barau Joel Amos (Sarkin Yaki) wajen shirya wannan makarkashiyar tare da sayen bindigogi a hannunsu domin kashe shi.

ADVERTISEMENT

Dogara ya shaida wa shugaban ‘yansandan cewa tunin kes din yake gaban DCP na sashin binciken na manyan laifuka ta rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, amma bisa girman lamarin ya ga dacewar sanar da shi domin fadada bincike, “Batu ne da ya shafi sace makamanku daga wasu jami’an da aka daura wa alhakin kula da makamai a wurin adanasu, shi Barau Joel Amos ko zai saya ko yana ma yana sayen bindigogi daga wajen jami’an.”

Dogara ya kara da cewa abun mamakin shine babu wani shawara a hukumance da ‘yansanda suka fitar dangane da wannan mummunar barazanar da ake yi wa rayuwarsu duk kuwa da cewa ana samun kesa-kesan garkuwa da mutane da kashe wasu ma musamman a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Dogaran sai ya buga misali da harin baya-bayan nan da wasu ‘yan bindiga suka kai kauyen Boto da ke gundumar Lere inda suka yi garkuwa da ‘yan uwan tsohon gwamnan Jihar Bauchi, Ahmadu Adamu Mu’azu da kashe wani, kan hakan ya nuna cewa akwai bukatar daukan matakan kan lamarin.

Ya ce irin wannan lamarin abun ne da ke bukatar gaggauta daukar matakin tare da cafke Barau Joel Amos domin zufafa bincike.

Hon. Yakubu Dogara ya kuma ce akwai matukar bukatar a binciki Barau Amos kan matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin tare da bincikar inda yake samun kudaden sayen makamai tare da bibiyar bayanan shigar kudi da fitar kudi na asusun ajiyarsa hadi da binciken wayarsa.

Ya ce akwai bayanan da suke da su da dama da ke nuna cewa shi Barau Joel Amos na da hannu a zarge-zarge da dama don haka akwai bukatar a tsare shi tare da zurfafa bincike a kansa.

Ya yi fatan cewa Shugaban na ‘yansanda ba zai yi wasa da wannan batun ba inda zai kaddamar da bincike domin tabbatar da inganci tsaro da kare rayuka da dukiyar jama’an yankin.

Dogara
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Ga Yadda Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.