• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
3 weeks ago
in Nishadi
0
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tamim Yahuza Abdullahi wanda aka fi sani da (TY) Shaba, a wata tattaunawar da ya yi da jarumar Kannywood Hadiza Gabon a cikin shirinta mai taken “Gabon’s Room Talk Show” ya bayyana abubuwa da dama da suka shafi rayuwarsa ta harkar fim da kuma ta zamowa mawaki wanda ya ce a yanzu ya daina waka sakamakon ganin da yayi cewa ba a nan Allah ya ajiye masa abincinsa ba.

Jarumin wanda ya shafe tsawon lokaci ana damawa da shi a masana’antar Kannywood a matsayin jarumi, mawaki, mai shirya fim da kuma mai daukar nauyi, ya bayyana tarihinsa inda yace shi haifaffen birnin Kano ne, wannan suna na T Y da akasarin mutane sukafi saninshi da shi ya samo asali ne tun daga lokacin kuruciya, na taso a gidanmu na iske yayana yana amfani da sunan D Y ma’ana Dauda Yahuza, hakan ya sa nima na takaita sunana domin ya zama kwatankwacin yadda ake kiran yayana saboda wannan inkiyar tashi a wancan lokacin ta na burgeni inji Tamim.

  • An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
  • Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Da yake amsa tambaya akan yadda ya samu Shaba a cikin sunanshi kuwa jarumin ya bayyana cewar sunan Shaba na sameshi ne a lokacin da nake karatu a Federal College Of Education (Technical) Bichi, a wancan lokacin akwai wani mawaki da ake kira Shaba Ranks to da yake ina matukar sha’awar wakokinsa sai ya zamana ina koyi da yanayin yadda yake waka har ma a wani lokaci aka shirya wani taro a makarantar sai na hau dandamali na rera wakokinsa cikin kwarewa.

To bayan na fito ne sai wata abokiyar karatuna ta kirani da wannan suna na SHABa cikin mutane, daga nan tun wancan lokacin sai ya zamana duk wani wanda bai san sunana ba yake kirana da Shaba, dangane da harkar waka kuwa ko da na shigo masana’antar Kannywood ni mawaki ne, domin kuwa na dade ina yin waka duk da cewa dai waka bata karbeni hannu biyu kamar yadda fim ya karbeni ba.

A kowane lokaci ina kiran kai na da wani wanda ko alama bashida basirar waka, hakan ya sa kacokan na hada kayana na koma na cigaba da yin fim a maimakon waka, ya kara da cewa, Shaba kuma ya bayyana wasu daga cikin abubuwan da suke ci wa masana’antar Kannywood Tuwo a kwarya kama daga rashin samun tallafi daga hukumomi da kuma rashin fadada ilimi a tsakanin jarumai, marubuta da masu shirya fina finan Hausa.

Labarai Masu Nasaba

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

A masana’antar Nollywood dake Kudancin Nijeriya, manyan masu kudinsu, sarakuna, hukumomi da gwamnatoci na iyakar kokarinsu wajen ganin masana’antar ta cigaba, ta hanyoyi daban daban da suka hada da kayan aiki, wajen daukar fim, fadada ilimi, tallace tallace da sauran tallafi da masana’antar ke bukata, a wasu lokutan ma akan daukesu har kasashen Turai wajen koyon aiki da kuma tallata hajarsu ga manyan dillalan fim a Duniya wanda ta wannan hanyar sai su samu manyan kudade.

T Y ya cigaba da cewa idan ana maganar masana’antar Kannywood ba haka abin yake ba, domin kuwa a nan yankin sai mai shirya fim ya nemi gida ko kamfanin da zai shirya fim din sa ya rasa, hakan zai sa ya je ya dauki Hotel ko wani gidan haya domin gudanar da aikinsa wanda yace ta haka ne zakaga fina finai suna kamanceceniya da juna saboda kusan komai da komai a waje daya akayi su sakamakon rashin wurare.

Mu a nan arewacin Nijeriya har yanzu ba a daukemu a matsayin wasu da zasu iya kawo cigaba kokuma su samar da aiyuka ga matasa ba, shi yasa ba duk taimako ake mana ba saboda a nasu tunanin babu wani abin cigaba da zamu iya kawowa, yanzu ga misali wanda yafi kowane mutum dukiya a nahiyar Afirika dan arewa ne kuma bahaushe, amma idan yanzu ana son ayi fim wanda za a taka rawar babban mutum kamar Dangote ba lallai bane hakan ta faru.

Saboda ba za a samu isassun manyan gidaje ko manyan motoci da za ayi amfani dasu a fim din ba duk da cewa akwai su da dama, don haka ina kira ga manyan masu kudinmu, mahukuntanmu, sarakuna da gwamnatocinmu su yi kokarin taimakawa wannan masana’antar ta Kannywood da ake shirya fina finai da harshen Hausa ta kowane fanni, hakan zai sa muyi gogayya da takwarorinmu na gida da ma na kasashen waje inji TY Shaba.

Daga karshe ya bukaci matasa da su kasance masu biyayya da hakuri, da kuma jajircewa wajen ganin burikansu sun cika, yace dole ne sai an sha wuya akan sha dadi, kuma duk wanda suka gani a cikin masana’antar Kannywood babu wanda ya shigo a matsayin mai kudi, kowa a talaka ya fara kafin ya zama abinda ya zama, don haka kuma idan kukayi hakuri komai zai zo ya wuce ba tareda wata tangarda ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Next Post

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

Related

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

4 days ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

4 weeks ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 month ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

1 month ago
Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

1 month ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

2 months ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.