• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sake haduwa da takwarorinsa na kasashen Kazakhstan da Kyrgyzstan da Tajikistan da Turkmenistan da kuma Uzbekistan a birnin Astana, inda suka halarci taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu, don bude sabon babin hadin gwiwar kasashensu. 

Haduwarsu a wannan karo ta biyo bayan wacce suka yi a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na farko da aka gudanar a birnin Xi’an na kasar Sin shekaru biyu da suka wuce. A wannan karo kuma, kasashen sun fitar da sanarwar Astana game da taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu, tare da rattaba hannu a kan yarjejeniyar kyakkyawar makwabtaka da abota da kuma hadin gwiwa na dindindin, baya ga shirye-shiryen hadin gwiwa har 110 da suka cimma.

  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Sai dai ma’anar taron ba ta tsaya ga wadannan nasarorin da aka cimma ba, abun da ya fi muhimmanci shi ne taron ya shaida inda za mu dosa musamman a yayin da duniyarmu ke fama da rashin tabbas da tashe-tashen hankula.

A yayin da shugaba Xi Jinping ke halartar taron, ya gabatar da jawabi, inda ya bayyana hadin gwiwar Sin da kasashen tsakiyar Asiya a matsayin “ruhin Sin da kasashen tsakiyar Asiya”, da ke “martaba juna da amincewa da juna da cin moriyar juna da kuma taimakon juna, da zamanantar da kowa ta tabbatar da ci gaba mai inganci.”

A bisa ruhin ne, Sin da kasashen nan biyar ke ta fadada hadin gwiwarsu, tare da karfafa hadin kansu don rungumar kyakkyawar makomarsu ta bai-daya. Idan mun duba, tun bayan taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na farko da aka gudanar a shekaru biyu da suka wuce, adadin cinikin da ke tsakanin Sin da kasashen nan biyar ya karu da kaso 35%, baya ga yadda suka inganta hadin gwiwarsu ta fannonin zuba jari da hakar ma’adinai ba tare da gurbata muhalli ba, da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha. Baya ga haka, a hukumance ne aka fara aikin gina layin dogon da ya ratsa kasashen Sin da Kyrgyzstan da Uzbekistan, kuma Sin da kasashen sun gina cibiyoyin al’adu a kasashen juna, kana Sin da Kazakhstan da kuma Uzbekistan sun cire wa al’ummomin juna bizar shiga kasashensu.

Labarai Masu Nasaba

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

A shekaru biyu da suka wuce, shugaban kasar Sin da takwarorinsa na kasashen nan biyar sun dasa wasu bishiyoyin ruman guda shida a birnin Xi’an, wadanda yanzu haka cike suke da furanni tare da alamanta hadin gwiwar kasashen mai cike da kyawawan nasarori, wadanda kuma suka shaida cewa, “hannu daya ba ya daukar jinka”, hada karfi da karfe ne zai kai ga inda aka dosa, kuma ba wanda ke iya cin nasara daga faduwar wasu, kuma za a iya tabbatar da nasara ga juna ne kurum idan aka zama tsintsiya madaurinki guda.

Yanzu haka, duniyarmu na fama da rikice-rikice da kariyar ciniki da ra’ayi na kashin kai da kuma siyasar nuna fin karfi. Amma bai kamata a mai da hannun agogon baya ba, kuma ba za a yarda da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummomin duniya ba, kana ‘yan Adam bai kamata su koma irin rayuwar da masu karfi ke cin zalin masu karamin karfi kamar yadda aka yi a baya ba.

Daga birnin Xi’an zuwa Astana, Sin da kasashen tsakiyar Asiya sun samar da ruhin da ya amsa tambayar da zamaninmu ya aza mana, wato “me ya faru a duniyarmu, kuma me ya kamata mu yi”, wanda kuma ya karfafa mana niyyar kiyaye adalci da cin moriyar juna da samun nasara tare, don kiyaye zaman lafiyar duniya da tabbatar da ci gaban kasa da kasa baki daya. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Next Post

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

Related

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

8 hours ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

1 day ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

1 day ago
Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

5 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

6 days ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

1 week ago
Next Post
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba

An Kashe 'Yan Ta'adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu - Hedikwatar Tsaro 

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.