Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Hafsoshin Sojin ƙasar nan bisa kyakkyawan sauyin da aka samu a fannin gudanar da aikin tsaro cikin shekaru biyu da suka gabata, wanda ya haifar da gagarumin cigaba da ba ya misaltuwa a fannin tsaron ƙasa baki ɗaya.
Mataimaki na Musamman ga ministan kan harkokin yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya ruwaito a cikin sanarwar da ya rattaba wa hannu cewa Idris ya yi wannan kalamin ne a ranar Alhamis, yayin wani taron tattaunawa da manyan shugabannin kafafen yaɗa labarai da sauran masu ruwa da tsaki, wanda aka gudanar a Hedikwatar Tsaro da ke Abuja, domin bikin cika shekaru biyu da naɗa Hafsoshin Soji da ke kan karaga yanzu.
- Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
- Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici
Ministan ya ce: “Bari in fara da isar da jinjina daga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR) ga Hafsoshin Sojin mu kan jajircewar su babu ƙaƙƙautawa, da ɗa’ar su da ƙaunar ƙasa wajen sauke nauyin da ke kan su.”
Idris, wanda shi ne ya jagoranci zaman, ya bayyana irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Babban Hafsan Tsaro da sauran Hafsoshin Sojin a matsayin mai tabbataccen tasiri da gamsasshen sakamako.
Ya ce: “Abin da muka gani ba wai kawai daƙile waɗannan barazanar ba ne, sai dai ma sake karɓe sararin ƙasar mu, da tunanin jama’a, da kuma a matakin aiki. Yanzu ‘yan Nijeriya za su iya tabbatar da cewa manyan hanyoyin mu sun fi samun tsaro ƙwarai idan aka kwatanta da ‘yan shekarun baya.”
Ya lissafa nasarorin da rundunonin sojin Nijeriya suka samu a sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da yankin Arewa-maso-gabas da gaɓar teku.
“Daga nasarar ragargaza sansanonin Boko Haram da ISWAP a Arewa-maso-Gabas, zuwa irin gagarumin farmakin da aka kai kan maɓoyar ‘yan bindiga a Arewa-maso-Yamma da Arewa-ta-Tsakiya; daga ingantaccen sintirin da sojin ruwa ke yi wanda ya rage yawan satar ɗanyen mai da rushe haramtattun matatun mai; zuwa luguden wutar sama da ba ya ƙarewa wanda ya tarwatsa hanyoyin sufuri da ɗaukar kaya na miyagun mutane — sakamakon da aka samu ba kawai abin burgewa ba ne, har ma abin kwantar da hankali ne.”
Ministan ya kuma jaddada muhimmancin rawar da kafafen yaɗa labarai suke takawa wajen gina ƙasa, yana mai roƙon su da su tallafa wa ƙoƙarin da rundunonin tsaro suke yi ta hanyar yaɗa nasarorin da suke samu.
Ya ce: “Ya kamata kafafen yaɗa labarai su riƙa bada rahoto ba kawai kan abin da ya zama ba daidai ba, har ma da abin da ake yi daidai. Ku riƙa hasko irin sadaukarwar da dakarun mu suke yi. Ku bada labaran cigaba da ake samu. Ku daidaita suka da cikakken bayani. Wannan shi ne ainihin aikin jarida bisa ƙwarewa.”
Ya bada tabbacin cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da tallafa wa rundunar soji ba kawai da kayan aiki kaɗai ba har ma da tsare-tsaren dabarun da za su inganta tattara bayanan sirri, haɗin gwiwar hukumomi, da walwalar ma’aikata.
Ya yaba wa Hafsoshin Sojin bisa shugabancin su na kishin ƙasa da samar da sakamako mai tasiri.
“Kun dawo da fata, kun ceci rayuka, kun kare martabar ƙasar mu, kuma fiye da komai ma, kun tunatar da mu ma’anar yi wa ƙasa hidima,” inji shi.
Ya kuma buƙaci kafafen watsa labarai da sauran masu ruwa da tsaki da su riƙa haska irin nasarorin da ake samu, yana mai cewa hakan yana da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa gwiwar jami’an tsaro.
“Ku lura da cigaban da ake samu kuma ku faɗaɗa yaɗuwar sa. Wannan na da matuƙar amfani ga ɗimbin dakarun mu da ke aiki dare da rana don kare ƙasar nan da samar da yanayin da duk ‘yan Nijeriya za su iya rayuwa, su yi aiki, su bunƙasa.”
Taron ya samu halartar Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, wanda Manjo Janar A.T. Jibrin (ritaya) ya wakilta; da Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa; da Manajan Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN), Malam Ali M. Ali; da Babban Daraktan Hukumar Gidajen Rediyon Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; da Babban Daraktan Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; da Shugaban da Shugaban Majalisar Ƙungiyar Masana Harkokin Yaɗa Labarai ta Nijeriya (NIPR), Dakta Ike Neliaku; da wakilan Hafsoshin Soji, da manyan shugabannin kafafen yaɗa labarai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp