A ƙalla matafiya 12 daga Zaria, jihar Kaduna aka kashe su a harin da ‘yan ta’adda suka kai a Mangu, jihar Filato a ƙarshen mako. Harin ya faru ne da ƙarfe 8 na dare ranar Juma’a lokacin da matafiyan ke kan hanyar zuwa ƙaramar hukumar Qua’an Pan domin halartar bikin aure.
An bayyana cewa sama da matafiya 18 ne suke cikin babbar motar bas ta Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) Zaria a lokacin harin. Direban bas, wanda ma’aikacin ABU ne, shi ma ya mutu a harin, yayin da wasu suka samu munanan raunuka, tuni an kai su asibiti.
- Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
- EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
Sheikh Suleiman Haruna, Imam na JIBWIS Mangu, ya tabbatar da cewa an ajiye gawarwakin takwas a babban Asibitin Mangu, yayin da ake neman sauran gawarwakin huɗu. “Jami’an tsaro sun duƙufa don gano waɗanda suka aikata wannan ta’asar,” in ji Imam.
Wanda ya tsira daga harin, Ibrahim Umar, ya ba da labarin cewa ‘yan ta’addan sun fara kashe direba, sannan suka kai hari ga sauran fasinjoji tare da kona motar. “Mun tsaya don yin tambaya ayi mana kwatance, amma ba zato ba tsammani suka kewaye mu suka fara kashe-kashe,” in ji Umar.
DSP Alfred Alabo, kakakin ‘Ƴansandan Filato, sun samu labarin faruwar lamarin kuma ana ci gaba da bincike. “Za mu fitar da cikakken bayani bayan an gama binciken,” in ji Alabo.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp