• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matakin kasar Amurka na amfani da jiragen yakinta samfurin “B-2 Spirit stealth”, wajen jefa bama-bamai kan cibiyoyin sarrafa sinadaran nukiliyar kasar Iran, karkashin shirin da aka yiwa lakabi da “Midnight Hammer”, ya kara ta’azzara halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya. 

Bayan da a fakaice Amurka ta nuna goyon bayanta ga hare-haren Isra’ila, sai kuma ta shiga kaddamar da hare-hare kai tsaye. Game da hakan, kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta shirya, ta fayyace yadda akasarin masu bayyana ra’ayoyi suka soki lamirin Amurka bisa hare-haren da ta aiwatar kan Iran, tare da sukar manufar kasar ta diflomasiyyar waje mai lakabin “Amurka gaban komai”, wadda a cewarsu ta haifar da mummunar ta’asa marar iyaka a Gabas ta Tsakiya.

  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Sakamakon jin ra’ayin jama’ar ya nuna cewa, kaso 91 bisa dari na masu bayyana mahangarsu, na ganin yayin da sassan kasa da kasa ke tsaka da kiraye-kirayen sassauta rikicin Isra’ila da Iran, matakin Amurka ya zamo tamkar watsawa wuta fetur, da jefa rikicin cikin wani yanayi da ka iya gagara a warware shi. A daya bangaren kuma, kaso 90 na masu bayyana ra’ayoyin na ganin hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin sarrafa sinadaran nukiliyar kasar Iran, sun yi matukar cin karo da dokokin MDD, da ka’idojin cudanyar kasashen duniya, kana ya keta ’yancin kasar Iran, da tsaro da ikon kare yankunanta.

Kazalika, kaso 77 bisa dari sun jaddada cewa, sarkakiyar yankin Gabas ta Tsakiya, ba za ta iya ba da damar wanzar da zaman lafiya mai dorewa a shiyyar da karfin soji ba, kana za a iya warware batun nukiliyar Iran, da tashe-tashen hankula tsakanin Isra’ila da falasdinawa ne kadai ta hanyoyin siyasa, da tattaunawa da hawa teburin shawarwari.

An gudanar da kuri’un jin ra’ayin ne ta dandalolin CGTN na Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha, inda mutane 10,472 dake kasashen ketare suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 12. (Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Next Post

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

Related

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

5 hours ago
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika
Daga Birnin Sin

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

6 hours ago
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

7 hours ago
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

8 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

9 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

10 hours ago
Next Post
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.