• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

by Alhaji Adamu Rabiu
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokacin da matasan Najeriya za su hallara a zauren babban taron matasa na kasa, daga 7 zuwa 21 ga Yulin 2025 a birnin Abuja, tambaya guda daya ce za ta mamaye tattaunawar a karkashin jigo mai taken “Gudanar da Mulki Da Shiga Harkokin Siyasa”. 

Ta yaya za mu dora siyasarmu a kan turba madaidaiciya, sannan kuma mu ceto dimokuradiyya daga hannun azzalumai a Nijeriya? A matsayina na mai gabatar da wannan kasidar tsarin manufofi zuwa kwamitin shirya taron, ban tsaya kan bayyana matsaloli kadai ba, na zo da cikakken shiri na ceto dimokuradiyyar wannan kasa. 

  • Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana
  • Yunkurin Matasan Nijeriya Na Son Zama Attajirai A Dare Daya Ta Hanyar Caca

Nijeriya na fama da mummunar matsalar rashin kyakkyawan fasilin siyasa, inda masu kudin haram ke karbe jam’iyyun siyasa, fagen siyasa ya zama cike da hadura da dungu, zabe ya koma yaudara, inda wanda ya ci zabe shi kadai ke cin moriyarta, ’yan gudun hijira sun rasa damar kada kuri’arsu, sannan hukumomin zabe na jihohi, sun zama karen farautar masu rike da madafun iko a jihohi, sannan suna yi wa gaskiya da rikon amana rikon sakainar-kashi. 

Wadannan matsaloli da wasu ma, na bukatar matasa su yi karatun ta-nutsu, su kuma  dauki matakin gaggawa; domin ceto Nijeriya daga hannun azzalumai, kana su kuma dora ta a kan turba madaidaiciya. 

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

Matsalolin Da Muke Fuskanta:                    

Bayan shekar 22 da kubutar da Nijeriya daga mulkin soja, dimokuradiyya na ci gaba da fama da rauni mai tsanani. Alamun cutar sun bayyana ne a cinikin baragurbin wakilai (delegates), amfani da kudin kasa da aka wawure ta hanyar haram wajen gudanar da yakin neman zabe, makudan kudin da ake ware wa Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), karancin yawan masu kada kuri’a, sayen kuri’u a bainar jama’a, tashin hankali yayin zabe, da kuma yaduwar fargaba, musamman a tsakanin matasa, cin amana na ’yan siyasa, canja sheka da zababbu ke yi, da dai sauran makamantansu.                                       

Asalin matsalar ita ce, rashin shiga cikin gudanar da gwamnati a siyasance (edclusion) na masu gaskiya da rikon amana, matasa, mata, masu fama da nakasa, ‘yan gudun hijira da jam’iyyun da ke da karamin karfi, duk sun kasance a wajen filin. 

Wannan ba kawai rashin adalci ba ne, har ma ya saba wa kundin tsarin mulki, kuma barazana ce ga zaman lafiya da ci gaban kasa. Idan ka duba, za ka fahimci cewa; dimokuradiyyarmu na hannun wasu tsirarun mutane da shugabannin jam’iyyu masu karfi, wadanda suka killace matasa da sauran ‘yan Nijeriya daga samun damar shiga siyasa ko a saurare su ko la’akari da tasu gudunmawar. Dimokuradiyyar cikin gida a jam’iyyu, abin dariya ne kawai, domin an mayar da zabe na cikin gida zuwa ciniki, wato ba ni kudi ga kuri’a. Inda a wani bangaren kuma, INEC na fuskantar kalubalen rashin ’yanci da rashin kwarin guiwar aiwatar da dokokinta. 

Har ila yau, ‘yan gudun hijira da sauran al’umma masu rinjaye ana ci gaba da ware su daga zabe. Haka nan, hukumar zaben jihohi, musamman yadda aka gani a zaben kananan hukumomi a Kaduna da Bauchi, sun zama wani kwafi da ya ci mutuncin dimokuradiyya. Wannan ya saba wa sassa da dama na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (Sashe 14(2)(a), 15(1), 40, 153(1)(f), 221, 318(1), da Jadawali na Bakwai), da Dokokin Kungiyar Tarayyar Afirka da kuma Majalisar Dinkin Duniya.   

 

Yadda Wannan Tsari Na Matasa Zai Taimaka Wajen Ceto Siyasarmu:

1-Yarjejeniya Ta kasa Don Siyasa Mai Inganci (National Charter for Inclusion): A samar da wata Yarjejeniya ta hadin gwiwa tsakanin Ma’aikatar Matasa ta Kasa, Kungiyar Gamayyan Jamíyyun Siyasa (IPAC), Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), Kungiyoyin Fararen Hula da Majalisar Matasa ta Nijeriya. Wannan yarjejeniya za ta kafa ka’idoji da dokokin da za su tilasta dimokuradiyya a cikin jam’iyyu, tabbatar da adalci wajen zabubbuka da kuma bai wa dukkannin jam’iyyun da suka shiga zabe damar ba da gudunmuwa wajen shugabanci a kowane mataki da kuma bai wa matasa, mata, ‘yan gudun hijira da kowa da kowa damar ’yancin tsayawa takara cikin adalci.  

2- Sauyi Mai Zurfi Ga Jam’iyyu da Tsarin Zabe: Ya zama wajibi jam’iyyu su bude kofa. A kafa dokar da za ta tilasta duk mai son tsayawa takara gabatar da “Tsarin Ayyuka” (Project Plans) kafin hawa kujera, sannan ya fitar da “Rahoton Karshe” (End-of-Term Reports), bayan barin gado ko da kuwa zai koma kuwa. A dakile kudin da ake nema marasa tushe daga masu neman takara, musamman na hukumomin zaben jihohi, (Misalin KAD-SIECOM). A tabbatar da cikakken amfani da Sashe na 7 na Kundin Tsarin Mulki da Dokar Zabe ta 2022.   

3- Runguman Dimokuradiyyar Dijital Hannu Biyu (Digital Democracy): A kafa “Cibiyar Dimokuradiyyar Dijital ta Kasa (NDDH)” da za ta sa ido, bayar da rahoto kai tsaye, sa ido kan kudin yakin neman zabe da tantance tsarin jam’iyyu. Za ta kuma ba da damar samun ilimin siyasa ta hanyar wasanni da fasahar zamani domin kara fahimta, rage rashin sha’awa daga matasa, da bunkasa ilimi da rikon amana. 

4- Karfafa IPAC Youth da Shirye-shiryen Fadakarwa: A karfafa Bangaren Matasa na IPAC (IPAC Youth Directorate) daga matakin kasa har zuwa jihohi, ta hanyar samar da doka, kasafin kudi da kuma tsarin aiki. Sannan, a dora musu alhakin wayar da kan jama’a a fadin kasar nan, musamman a tsakanin wadanda aka ware daga siyasa. 

Me Za Mu Samu Idan An Bi Wannan Hanya? Za mu samu dimokuradiyya mai inganci da kuma tsabta, inda matasa, mata, masu fama da nakasa (PWDs) da ‘yan gudun hijira (IDPs) za su samu bakin fada kuma a ji a cikin siyasa da shugabanci. Za a samu karancin tashin hankali a lokacin zabe, raguwar sayen kuri’a da ingantaccen ilimi da wayewa a tsakanin jama’a.  Za kuma a samu jam’iyyu masu gaskiya da amana da kuma shugabanci na kwarai da ci gaban kasarmu Nijeriya. 

 

Matakan Aiwanar Da Wannan Tsari: 

Mataki na 1: Rubuta NSPPC tare da dukkan masu ruwa da tsaki.

Mataki na 2: Kafa tsarin dubawa tsakanin INEC, IPAC da CSO.

Mataki na 3: Kaddamar da NDDH da kayan aikin ilmantarwa.

Mataki na 4: Gyaran Dokar Zabe, domin shigar da wadanan al‘amura da muka gabatar a sama da sauran bukatu. 

Kafin Mu Kammala: Makomar dimokuradiyyar Nijeriya na cikin hadari. Ba za mu iya ci gaba da kallon halin da ake ciki ba na rashin adalci, cin amana, zangon kasa ga kasa da al’úmarta. 

Yazama wajibi mu yi amfani da karfin matasa, domin ceto Nijeriya daga bakin kuraye. Kirkire-kirkire da bukatar rikon amana, su ne maganin cutar da dimokuradiyyarmu ke fama da ita. 

Wannan tsari nawa na zuwa ne daga gwanancewa da aiki da IPAC, shirye-shiyen fitar da sakwanni ta ‘Bakondare Speaks’, wallafa rubuce-rubuce a manyan jaridu kamar su Premium Times, Daily Trust, Guardian, Punch, Banguard, Thisday , Leadership (A hausance da turanci)) da kuma shiga ayyukan siyasa masu tsafta da kuma alaka da kungiyoyi masu muhimmanci na siyasa.   

Yanzu ne lokacin sauyi! Muryar matasa ya kamata ta koma tsakiya wajen tsara manufofi da aiwatar da su. Yakamata dimokuradiyyar Nijeriya ta amfani kowa da kowa ba wasu ba kawai! 

Kafin rahoton karshe na wannan taro ya isa ofishin Shugaban Kasa ranar 12 ga Agusta, 2025 (Ranar Matasa ta Duniya), ina kira da babbar murya da fatan alheri ga duk dan Nijeriya da kuma dukkan wakilai da su rungumi wannan tsari. Ina kuma kira ga ’yan majalisa da masu zartarwa da su aiwatar da shi, domin ci gaban Nijeriya da kuma amfanin masu zuwa nan gaba. Yanzu ne lokacin daukar mataki na hakika da Jarumta! Allah ya yi mana albarka, ameen.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DimokuraɗiyyaMatasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Next Post

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Related

Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

5 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

9 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

10 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

24 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

1 day ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

1 day ago
Next Post
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.