ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin Matasan Nijeriya Na Son Zama Attajirai A Dare Daya Ta Hanyar Caca

by Leadership Hausa
1 year ago
Caca

Ana samun dinbin kudaden shiga masu yawa a fannin a kasar nan, musamman duba da yadda ake ci gaba da yadda wasu matasan kasar, ke ci gaba da fuskatar kangin matsin tattalin arziki, hakan ya tilastawa wasu matasan kasar, rungumar dabi’ar Caca, bisa nufin zamowa attajirai a dare daya.

Rahoto da Mujallar Lancet, ta wallafa, ta yi gargadin cewa, wannan dabi’ar na ci gaba da zama zamowa wata barazana ga fannin kiwon lafiyar masu yin dabi’ar a fadin duniya, musamman a Nijeriya, ganin yadda ake gudanar da wannan harkalar har a hanyar a wayoyin tafi da gidanka da kuma ta yanar Gizo.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Sin Ta Bayyana Wani Shiri Na Bunkasa Kiwon Lafiya

Duba da cewa, masu yin wannan dabi’ar akasarinsu, su kan kasance a lokacin da suke kan gudanar da ita, suna yawan zukar Taba Sigari ko kuma yawan kwankawadar Barasa, saboda kara zurfin yin tunani, duba da cewa, masu yin dabi’ar da suka kai miliyan 450, za su iya fuskatar larurar ta kwakwalawa.

ADVERTISEMENT

A saboda hakan ne, wasu kwararru, suka bayar da shawarar da a kakaba sharuddan kan yin tu’ammali da Taba Sigari da Barasa.

Bugu da kari, dangane da wani rahoto na alkaluman Statista na duniya da kuma sirrin gudanar da kasuwanci suka fitar, sun nuna cewa, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 60, masu shekaru daga 18 zuwa 40, suka rungumi wannan dabi’ar.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Kazalika, a wani binciken kwanan baya na gama gari kan yawan alummar kasar, ya gano cewa, kaso 53 na wasu matasan kasar, a kullum suna rungumar wannan dabi’ar.

Sai dai, muna sane da cewa, wasu ‘yan Nijeriya, na kallon yin cacar tamkar wata aba ce, ta nishadi kawai, amma wasu bincike sun bayyana cewa, wani dan bangere na mutanen da ke yin cacar ne kawai, ke samun a cacar, inda akasarin sauran, ke tabka asarar kudadensu da suka zuba a cikin cacar.

An dai jima ana yin caca a kasar, wadda a shekarun baya, ake yi mata wani kallon kan abinda bai dace ba, kamar dai yadda Coci ta alakanta ta, a matsayin hanyar yin arzikin dare daya

Idan za a iya tunawa, bangare na 22 na sashe 236 na kundin dokar aikata manyan laifuka na 1990, Gwamnatin Tarayya ta halasta wasu nau’uka na yin caca, musamman domin ta samar da kanta, kudaden shiga.

Dokar ta fayyace tsakanin wasan kwarewa wanda yake an halasta da kuma wani wasan, na neman sa a, wanda aka haramta.

Wasu nau’ukan na cacar da aka halasta, sun hada da, cacar da ake sayen wani Tikiti domin shiga gasar zamowa Zakara kan wani abu da aka sanya kamar mota ko wani gida da sauransu.

Amma abin takaici, hakan ya sanya cacar ta kara karbuwa ga wasu alummar gari, musamman a tsakanin yaran da suke da kanannan shekaru.

Kazalika, mun fi lura da akasarin nau’ukan cacar da ake yi a kasar, misali wacce a yanzu ake yi kasar kamar ta gasar ta Kwallon Kafa da sauransu, da ake yi, a kafar Internet.

An yi hasashen cewa, rashin aikin yi, sun arzirta a dare daya, matsain tattalin arziki, su ne, kusan hummulhaba’isin da ke sanya wasu mutanen kasar, musamman matasa ke rungumar wannan halin, inda kuma hakan, ke kara haddasa, aikata manyan laifuka.

Muna damu makuka kan yadda wannan halin, ke kara tarwatsa, tarbiyar wasu matasan kasar, da suka rungimi wannan dabi’ar.

A saboda haka, akwai bukatar Gwamnatin Tarayya, ta dauki matakin kan wannan batun.

Fanin cacar gasar wasa ta Nijeriya, ta kasance a kan gaba a Afirka, duba da yadda a kasuwar a 2023 aka samu ribar da kai ta akalla dala biliyan biyu,

Kazalika, duba da yadda a fannin ake samun sama da tiriliyan uku ko kuma sama da haka, cacar gasar wasa ta Nijeriya, sama da shekarun da suka wuce, wannan fannin, sai kara tumbatsa yake yi kasar, wanda haka na faruwa ne, saboda matsin tattalin arziki, karuwar matasa marasa aikin yi da kuma kara bunkasar yin amfani da wayoyin tafi da gidanka.

Ana dai kara ci gaba da samun irin wadannan shagunan da ake gudanar da irin wannan cacar ta gasar wasanni kusan ako wanne tituna da kuma a dandalin sada zumunta, wanda hakan, ya bai matasan kasar da damar, rungumar dabi’ar ta caca, musamman domin su samar wa kansu, da kudaden shiga,

Zamu iya cewa, mun jahilaci cewa, kasancewar yanayin matsalin tattalin arziki da Nijeriya ke fuskanta ne, ya hadda samun karin guraren da ake gudanar da gasar ta cacar wasanni.

A cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa NBS, samun karuwar matasa marasa aikin yi a kasar, ya sanya su daukar matakan da suke ganin ya dace da su, domin su samarwa da rayuwarsu mafita, musamman yadda suke kara rungumar cacar ta gasar wasanni, da suke mata kallon mataki na zuba hannun jari.

An kiyasata cewa, a wannan fannin, ana samaun akalla Naira tiriliyan uku a shekara, wanda kuma ake kara samun ‘yan kasuwa na tallata hajojinsu ta hanyar amfani da kafar sada zumunta, daukar nauyin tallace-tallacen, da suka samu amincewar wasu fitattu.

Wannan ya nuna yadda rahoton Mujallar Lancet ya bayyana matasan da suka rumgumi cacar ke shafe sa’oi 24 suna gudanar da cacar, wadda kuma ke shafar lafiyarsu da barnatar da kudaden da suke yi.

A bangaren mu, tsawon lokacin da ake ci gaba da fuskanta na kangin matsin tattalin arziki a kasar wanda hakan, ya tilatsa wasu matasan yin cacar ta wasanni, abin damuwa ne.

Bugu da kari, yadda wannan batun ke shafar tabin hankalin matasa da ke yin dabi’ar abin damuwa ne, musamman ganin yadda kwararru a fannin kiwon lafiyar ‘yan Adam suka yi gargadin cewar kara samun matasa masu yin dabi’ar a kasar, na kara jefa matasan a cikin matukar damuwa, inda har wasu matasan saboda fusatar rashin samun nasara a dabi’ar, suke kashe kansu ko kuma rungumar tu’ammali, da kayan maye.

Mai makon su rinka zuba kudaden su a halastattun sana’oi, amma sai buge za zuba kuaden, a cacsar gasar wasannin

Duk da ikirarin da irin wadannan kamfanonin na cacar gasar wanni ke yi cewa, suna samar da nishadi da damar samar da ayyukan yi ga matasan ne, ammu mu dai, mun yi ammanar cewa, suna dai kawai amshe ‘yan kudaden matasan ne.

Babu wata tamtama, akwai bukatar a kakabawa fannin da irin wadannan kamfaonin na cacar gasar wasannin, tsauraran matakai.

Kazalika, akwai matukar bukatar Hukumar sa ido kan irin caca ta kasa NLRC wacce kuma ke sa ido kan cacar gasar wasanni ta kara karfafa dokokin yin gasar cacar ta wasanni tare da daukar matakan da suka kamata, ciki har da sanya dokar tallace-tallace da iyakance yawan kudaden da ake zubawa a cikin cacar, kamar dai, yadda ake yi wasu kasashen duniya.

Hakazalika, ya zama wajibi, Gwamnatocin Jihohi su tashi tsaye, wajen samar da tsare-tsaren da matakai da za su hana matasa shiga cikin dabi’ar.

Idan har mahukunta a kasar ba su samar da daukin da ya dace ba, yunkurin matasan na son arzircewa a dare daya, za ta ci gaba da kasancewa, wanda hakan kuma, zai shafi makoyar matasan.

Caca
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Waraka Daga Bashin Ketare

Waraka Daga Bashin Ketare

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.