• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada
3 months ago
in Wasanni
0
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gasar cin Kofin Duniya ta kungiyoyi ko kuma FIFA Club World Cup da a yanzu ake gudanarwa a kasar Amurka za ta bai wa tawagogin Afirka hudu da za su buga gasar karin damar bajakolin ‘yan wasan Afirka da kuma irin yadda kasashen na Afirka suke kokarin ganin sun fara goga kafada da kafada da manyan kungiyoyi a nahiyar Turai da kuma kudancin Amurka.

Kungiyar Al Ahly ta Masar da ta lashe kofin Champions League na Afirka sau 12, da Mamelodi Sundowns ta Afirka ta Kudu, da Wydad Casablanca ta Morocco, da Esperance ta Tunisia, su ne za su nemi murkushe takwarorinsu na Turai da sauran nahiyoyin duniya da a yanzu suke fafatawa a gasar da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta shirya a karon farko.

  • Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?
  • Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Babu wata kungiya daga Afirka da ta taba lashe kofin gasar ta Club World Cup a tarihi, inda biyu ne kawai suka taba kai wa wasan karshe a karo 20 na gasar. Amma yanzu akwai ladan da za a samu – jimillar abin da za a bayar ya kai Dala biliyan daya, inda aka ware Dala miliyan 475 don bai wa wadanda suka fi kokari. Duk da cewa FIFA ta kara yawan wasannin da aka saba bugawa duk da yawan wasannin da ke gaban kungiyoyi, kocin Esperance Maher Kanzari ya ce “dama ce” ga ‘yanwasa su bayyana kansu.

Duka kungiyoyin Afirka da za su buga gasar ta Kofin Duniya za su samu ladan akalla Dala miliyan 9.55 – irin wadannan wakilai daga Asiya da Arewacin Amurka da Amurka ta Tsakiya za su samu. Wannan adadi ya ninka Dala miliyan hudu da Palmiras ta samu bayan lashe kofin zakarun nahiyar Afirka.

Duk da haka, ladan da kungiyoyin Afirka za su samu shi ne mafi kankanta. Wakilan Kudancin Amurka shida za su samu ladan Dala miliyan 15.21, yayin da kungiyoyin Turai 12 za su samu kudi daga Dala miliyan 12.81 zuwa 38.19.

Labarai Masu Nasaba

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

Nasarar da kungiya ta samu a matakin rukuni za a ba ta Dala miliyan biyu, canjaras kuma miliyan daya, wadda ta cinye kofin kuma za ta samu ladan Dala miliyan 40. Ganin yadda kungiyoyin Turai suka mamaye gasar, Afirka na fatan samun karin dama a nan gaba, ma’ana a Karara nahiyar Afirka yawan kungiyoyin da za su dinga wakiltar ta.

Wasu na fatan kungiyoyin Afirka da ke cikin gasar za su ja hankalin duniya zuwa nahiyar ko da kuwa gasarta ta zakaru ba ta iya yin hakan ba, da kuma kawo musu kudi idan aka kwatanta da takwarorinsu.

Sabuwar gasar African Footbal League da hukumar CAF ta kaddamar a 2023 ba a sake yin ta ba, duk da irin rigingimun da aka yi lokacin da aka fara ta, mai tawaga hudu wadda kungiyar Sundowns ta lashe.

Kungiyar Pretoria da shugaban hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF, Patrice Motsepe ya mallaka, ta kafa kanta a matsayin jagora a harkar kwallon kafar Afirka – ita ta lashe kofunan gasar Afirka ta Kudu tara na baya-bayan nan.

Sundowns za su kara da Ulsan HD da Borussia Dortmund da Fluminense a Rukunin F, abin da wani magoyi kwallon kafa ya ce zai taimaka wajen nasararta a gasar ta Club World Cup.

Lokacin gudanar da gasar Club World Cup ya shafi harkokin wasa a Afirka, ta yadda sai da aka matsar da lokacin gudanar da gasar Kofin kasashen Afirka wato AFCON 2025 daga watannin Yuni da Yuli zuwa karshen shekarar ta 2025. Tuni kungiyar kwararrun ‘yankwallo ta duniya ta shigar da kara a shekarar da ta gabata kan abin da suka kira “nuna karfin iko” da FIFA ta yi wajen fadada gasar, amma kuma duk da haka ba a dakata ba.

Danwasan Nijeriya na AC Milan Samuel Chikwueze ya ce kungiyarsa ba za ta buga gasar ba, amma duk da haka yawan wasannin da za su buga sun yi yawa. ‘Yan wasan dai sun yi korafin cewa lokaci daya da ‘yanwasa za su huta shi ne daidai lokacin da suka saka gasar. ‘Yan wasan sun bayyana cewa abu ne mai wahala buga wasanni masu yawa domin mutum zai gajiyar da kafufuwansa da tunaninsa ta yadda ma ba zai ji dadin buga wasan ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaDuniyaƘwallon Ƙafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Next Post

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Related

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5
Wasanni

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

2 days ago
An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
Wasanni

An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m

3 days ago
Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata
Wasanni

Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

4 days ago
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
Manyan Labarai

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

4 days ago
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
Manyan Labarai

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

5 days ago
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

6 days ago
Next Post
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya -  Shugaban ƘasaTinubu

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

September 27, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

September 27, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.