• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

by Muhammad
3 days ago
in Manyan Labarai
0
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a matsayin jagoran siyasarsa, wanda ya ƙarfafa masa guiwa har ya tsaya takarar gwamnan Kaduna.

A sakon ta’aziyyarsa, El-Rufai ya ce Buhari ya tsaya tsayin daka don ci gaban Nijeriya, ya bayar da gudummawa mai tsoka a matsayinsa na soja kuma shugaban ƙasa na mulkin soja da kuma zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.

  • Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida
  • Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

El-Rufai ya ce Buhari ya kasance jarumi mai juriya wanda duk da tsige shi daga mulki a 1985, ya dawo kuma ya lashe zaɓe a 2015.

“Ko da yake bai cika magana ba, yana da natsuwa da barkwanci. Yana da hali mai sauƙi da ya sa talakawa ke ƙaunarsa, saboda suna ganin shi mutum ne mai gaskiya da amana.”

“Ko bayan faɗuwarsa a zaɓen shugaban ƙasa sau uku, ya sake tashi suka kafa jam’iyyar APC a 2013, wanda ya kayar da shugaban ƙasa mai ci a 2015. Ya kuma miƙa mulki cikin nasara a 2023, wanda hakan ya kafa tarihi.”

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Ya ƙara da cewa ya samu damar yin aiki da Buhari a jam’iyyar CPC bayan zaɓen 2011, inda Buhari ya sa shi ya jagoranci kwamitin farfado da jam’iyyar. Kwamitin ne ya ba da shawarar haɗakar CPC da ACN da sauran jam’iyyu don tunkarar zaɓen 2015.

“Shugaba Buhari shi ne jagoran siyasa ta. Shi ya karfafa min guiwa na tsaya takarar gwamnan Kaduna. Ya halarci ƙaddamar da kamfe ɗina a watan Nuwamba 2014, kuma ya tsaya min har na kai ga nasara. Ina godiya sosai da goyon bayansa a lokacin gwamnatina, har da damar da na samu na tattaunawa da shi a kowane lokaci, ko da kuwa muna da saɓani a wasu manufofi.”

El-Rufai ya roƙi Allah Ya gafarta wa Buhari, Ya sanya shi a Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa, musamman Hajiya Aisha Buhari da ’ya’yansa, hakurin rashinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariEl-RufaiKadunaLandanRasuawaRasuwar Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

Next Post

Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

Related

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

2 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

9 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

11 hours ago
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu
Manyan Labarai

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

11 hours ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

1 day ago
Next Post
Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da 'Yan Nijeriya Ta'aziyyar Rasuwar Buhari

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

July 17, 2025
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

July 17, 2025
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

July 17, 2025
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

July 17, 2025
Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

Alkaluman Tattalin Arzikin Sin A Rabin Farkon Bana Sun Zarce Hasashen Da Aka Yi

July 17, 2025
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

July 17, 2025
Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.