ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida

by Muhammad
11 months ago
Babangida

Tsohon shugaban ƙasa, Janaral Ibrahim Badamasi Babagana ya bayyana alhininsa bisa rasuwar abokinsa kuma tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu ranar Lahadi 13, ga Yulin 2025 a wani asibiti da ke birnin Landan.

Babangida ya ce: “Ina cike da alhini da juyayi na samun labarin rasuwar abokina, ɗan’uwana, abokin karatuna a makarantar soja, kuma abokin gwagwarmayar gina ƙasa, Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, GCFR.”

  • Sarkin Musulmi, Ya Yi Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari
  • Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

“Mun fara haduwa da shi a shekarar 1962 lokacin da muka shiga Kwalejin Horan Sojoji ta Nijeriya da ke Kaduna. Tun daga wancan lokaci, Muhammadu Buhari ya fara bambanta kansa da saura, saboda mutum ne mai ƙarfin zuciya da tsarin rayuwa, kuma ɗan kishin ƙasa mai ƙaunar ci gaban Nijeriya. Mun sha wahala tare, mun kuma yi faɗi-tashi tare. Ƙaunar ƙasa da ƙwarewa a aiki su ne suka haɗa mu wuri guda, ba kawai aikin soji ba.” In ji Babangida

ADVERTISEMENT

Janar Babagida ya ci gaba da cewa: “A cikin aikinmu, ƙaddara ta sa kowannenmu ya shugabanci Nijeriya a lokuta daban-daban da yanayi daban. Amma a kowane lokaci, Buhari ya kasance mai kishin gaskiya da bin tsarin mulki da martabar shugabanci. Ya yi wa Nijeriya hidima da amana da jajircewa ko da kuwa a wasu lokutan wasu ba su fahimce inda ya dosa ba.”

“Bayan aikin soji, na san shi a matsayin mutum mai tsoron Allah, wanda yake da nutsuwa da riƙo da addininsa, kuma yana rayuwa da tawali’u da rayuwa akan manufa. Duk da cewa ba koyaushe ra’ayinmu yake zuwa ɗaya ba, kamar yadda yake a tsakanin ‘yan uwa, amma ban taɓa shakkar gaskiyarsa ko kishin ƙasarsa ba,”

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

“Rasuwar Buhari ba kawai rasa tsohon shugaban ƙasa ba ne, ko shugaban da aka zaɓa sau biyu a mulkin dimokuraɗiyya ba. Rasa shi babban rashin mutum ne wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen haɗa tsohuwar Nijeriya da sabuwar jamhuriya. Ko a lokacin da ya yi ritaya, ya kasance abin koyi da nagarta da gaskiya ga mutane da dama.”

A ƙarshe tsohon shugaban ƙasar, ya yi addu’a ga marigayi Buhari tare da miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga matarsa Aisha da ‘ya’yansa, da jikokinsa da dukkan jama’ar Nijeriya da ya yi wa hidima. “Allah ya gafarta masa, ya karɓi ayyukansa na alheri, ya kuma sanya shi a Aljannatul Firdaus.” In ji Janar Ibrahim Badamasi Babangida, tsohon shugaban Nijeriya, a cikin wani sakon ta’aziyya da ya aike a ranar Lahadi 13, Yuli 2025.

Babangida
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar
Manyan Labarai

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi
Manyan Labarai

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni
Manyan Labarai

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Next Post
Chelsea Ta Kafa Babban Tarihi Bayan Lashe Kofin Duniya Na Ƙungiyoyi

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.