ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Rashin Jagora, Buhari Ne Ya Ƙarfafa Min Guiwa Na Yi Takarar Gwamna A Kaduna — El-Rufai

by Muhammad
11 months ago
El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana marigayi tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a matsayin jagoran siyasarsa, wanda ya ƙarfafa masa guiwa har ya tsaya takarar gwamnan Kaduna.

A sakon ta’aziyyarsa, El-Rufai ya ce Buhari ya tsaya tsayin daka don ci gaban Nijeriya, ya bayar da gudummawa mai tsoka a matsayinsa na soja kuma shugaban ƙasa na mulkin soja da kuma zaɓaɓɓen shugaban ƙasa.

  • Rasuwar Buhari: Na Yi Rashin Ɗan’uwa, Aboki, Ɗan Ƙasa Nagari —Babangida
  • Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

El-Rufai ya ce Buhari ya kasance jarumi mai juriya wanda duk da tsige shi daga mulki a 1985, ya dawo kuma ya lashe zaɓe a 2015.

ADVERTISEMENT

“Ko da yake bai cika magana ba, yana da natsuwa da barkwanci. Yana da hali mai sauƙi da ya sa talakawa ke ƙaunarsa, saboda suna ganin shi mutum ne mai gaskiya da amana.”

“Ko bayan faɗuwarsa a zaɓen shugaban ƙasa sau uku, ya sake tashi suka kafa jam’iyyar APC a 2013, wanda ya kayar da shugaban ƙasa mai ci a 2015. Ya kuma miƙa mulki cikin nasara a 2023, wanda hakan ya kafa tarihi.”

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

Ya ƙara da cewa ya samu damar yin aiki da Buhari a jam’iyyar CPC bayan zaɓen 2011, inda Buhari ya sa shi ya jagoranci kwamitin farfado da jam’iyyar. Kwamitin ne ya ba da shawarar haɗakar CPC da ACN da sauran jam’iyyu don tunkarar zaɓen 2015.

“Shugaba Buhari shi ne jagoran siyasa ta. Shi ya karfafa min guiwa na tsaya takarar gwamnan Kaduna. Ya halarci ƙaddamar da kamfe ɗina a watan Nuwamba 2014, kuma ya tsaya min har na kai ga nasara. Ina godiya sosai da goyon bayansa a lokacin gwamnatina, har da damar da na samu na tattaunawa da shi a kowane lokaci, ko da kuwa muna da saɓani a wasu manufofi.”

El-Rufai ya roƙi Allah Ya gafarta wa Buhari, Ya sanya shi a Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa, musamman Hajiya Aisha Buhari da ’ya’yansa, hakurin rashinsa.

El-Rufai
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Next Post
Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da ‘Yan Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

Shugaban ECOWAS Julius Bio, Ya Yi Wa Tinubu Da 'Yan Nijeriya Ta'aziyyar Rasuwar Buhari

LABARAI MASU NASABA

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.