ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
5 months ago
Lamine

Ma’aikatar kare hakkin jama’a ta Sifaniya ta bukaci ofishin mai shigar da kara na kasar da ya binciki dan wasan gefe na Barcelona Lamine Yamal bayan da aka ce ya dauki hayar gajerun mutane zuwa wajen bikin cikarsa shekaru 18 da haihuwa, Lamine Yamal ya shirya liyafa a ranar Lahadi a wani wajen da ya dauka haya a Olibella, wani karamin gari mai tazarar kilomita 50 arewa maso yammacin Barcelona, a cikin wadanda suka halarci bikin akwai masu amfani da shafukan YouTube, mawaka da abokan wasansa a Barcelona da dama.

Ana zargin Lamine Yamal ya dauki hayar gungun masu wasan nishadi da ake kira da (Dwarf) wato wadanni domin nishadantar da mahalarta taron, wani abu da kungiyar mutanen da ke fama da ciwon Achondroplasia da sauran matsaloli na kashi (Skeletal Dysplasias) a kasar Sifaniya (ADEE) suka kira da abin da ba a yarda da shi ba a karni na 21, Darakta Janar na Nakasassu, wani bangare na Ma’aikatar Kare Hakkin Jama’a, ya ce kungiyar ADEE ta shigar da karar akan Yamal.

  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
  • Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike

Saboda haka, Darakta Janar din ya bukaci ofishin mai gabatar da kara da ya yi bincike domin sanin ko an tauye hakkokin nakasassu ko kuma an keta hakkin nakasassu, ADEE ta ce “Ta fito fili ta yi Allah wadai da daukar wadannin da ke da ra’ayin mazan jiya a matsayin wani bangare na nishadantarwa, kuma ta ce za ta dauki matakin shari’a saboda wannan ka iya zama wata hanya ta nuna wariya a tsakanin nakasassu da sauran mutane a kasar ta Sifaniya da ake yawan samun kararraki na nuna wariyar launin fata,” in ji shi.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce “Wadannan ayyuka ba wai kawai sun saba wa dokokin da ake da su a yanzu ba, har ma da muhimman ka’idojin da’a na al’ummar da ke neman daidaito da mutuntawa, akwai doka game da hakkin nakasassu da ta haramta ayyukan nakasassu a fili kamar aikata ayyukan nishadi a wajen taron jama’a ko wajen bukukuwa, wadanda ake amfani da nakasassu ko wasu masu rashin lafiya wajen yin izgili ko ba’a, wanda hakan ya matukar saba wa dokar mutunta dan’Adam,” in ji sanarwar.

 

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco
Wasanni

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey
Wasanni

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Tauraruwarsu Za Ta Haska A AFCON

December 20, 2025
Next Post
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.