• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

by Abubakar Sulaiman
2 days ago
in Kasashen Ketare, Manyan Labarai
0
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙasar Iran ta zargi Birtaniya, Faransa, da Jamus da karya alƙawuran da suka ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar JCPOA da aka cimma a shekarar 2015, bayan ƙasashen uku sun yi barazanar dawo da takunkumi karya tattalin arziƙi ga ƙasar.

An ƙulla yarjejeniyar ne domin taƙaita shirye-shiryen nukiliyar Iran a maimakon sassauta mata takunkumi, sai dai yarjejeniyar ta fara rushewa ne bayan Amurka ta fice daga ciki a 2018 a lokacin shugaba Trump, inda ta dawo da manyan takunkumin karya tattalin arziƙi kan Iran.

  • Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa
  • Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Ko da yake Turawan sun yi alƙawarin bin yarjejeniyar, da ƙoƙarinsu na rage wa Iran raɗaɗin takunkumin Amurka bai haifar da ɗa mai ido ba. Manufofin kuɗi da Turai ta ƙaddamar domin taimaka wa Iran sun gaza, kamfanoni daga yammacin duniya kuma sun fice daga Iran, lamarin da ya tsananta matsin tattalin arziƙi a ƙasar. Iran na zargin ƙasashen Turai da cewa sun tsaya ne a kan magana kawai ba tare da aiki ba.

A ranar Litinin, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baqaei, ya soki Turai bisa abin da ya kira da “gazawa da sakaci” wajen aiwatar da yarjejeniyar, yana mai kiran barazanar da suke yi a yanzu da “rashin adalci” kuma “cike da son zuciya”. Wannan na zuwa ne bayan Turawan sun nuna damuwa kan matakin da Iran ta kai na inganta sinadarin uranium zuwa kashi 60% wanda hukumar IAEA ta ce ya ninka ƙima mafi girma da yarjejeniyar JCPOA ta amince da shi wato 3.67%.

Ƙasashen Birtaniya, Faransa da Jamus na shirin amfani da tsarin “snapback” na Majalisar Ɗinkin Duniya wanda ke ba su damar dawo da takunkumi idan aka samu Iran da laifin karya yarjejeniya. Baqaei ya kare matakin Iran da cewa ƙasar ta fara rage bin yarjejeniyar ne bayan ficewar Amurka da gazawar Turai wajen cika alƙawari, yana mai cewa duk matakan Iran sun yi daidai da sharuɗɗan yarjejeniyar dangane da martani na musaya.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Wannan rikici ya ƙara jaddada gazawar yarjejeniyar ta JCPOA kuma ya tayar da ƙarin shakku kan yiwuwar dawo da tattaunawar diflomasiyya don taƙaita shirye-shiryen nukiliyar Iran. Tunda kowanne ɓangare ke jifan ɗayan da laifi, yanzu dai alamar dawowa ga yarjejeniyar 2015 na ƙara dusashewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmericanEuropeanIranUSA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴan Bindiga Sun Tafka Gagarumar Sata A Bauchi, Sun Tafi Da Mutane 4

Next Post

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Related

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

2 hours ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

3 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

4 hours ago
Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
Manyan Labarai

Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21

7 hours ago
Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
Manyan Labarai

Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro

11 hours ago
Rayuwata Na Cikin Hatsari, A Dawo Min Da Jami’an Tsarona – Natasha 
Manyan Labarai

Rayuwata Na Cikin Hatsari, A Dawo Min Da Jami’an Tsarona – Natasha 

12 hours ago
Next Post
Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

Tsoffin Ƴansanda Sun Fara Zanga-Zangar Ƙuncin Rayuwa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

July 22, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Shawarwari Da Tattaunawa

July 22, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7

July 22, 2025
Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu

July 22, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

July 22, 2025
Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

Karin Maganar Sinawa: Koyar Da Su Ya Fi Bayar Da Kifi

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.