• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

by Abubakar Sulaiman
1 day ago
in Wasanni
0
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabon Darakta Janar na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, Ahmed Musa, ya bayyana cewa samun mukamin shugabanci a ƙungiyar ba zai hana shi ci gaba da taka leda ba. A wata hira da yayi da RFI Hausa, Musa ya bayyana cewa kasancewarsa tsohon ɗan wasan Pillars tun lokacin ƙuruciya ne ya sanya zuciyarsa ke cike da ƙauna da kishin ƙungiyar. Ya ce yana jin ciwo idan ƙungiyar ta shiga halin rashin nasara, don haka zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa.

Ahmed Musa ya kuma jaddada buƙatar samun cikakken goyon bayan magoya bayan Kano Pillars domin a samu damar farfaɗo da martabar ƙungiyar a fagen ƙwallon ƙafa. A cewarsa, ƙungiyar na buƙatar haɗin kai da jajircewar kowa domin samun nasara, musamman a wannan sabon zamani da ƙwallon ƙafa ke ƙara fuskantar ƙalubale.

  • Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

A cikin kwanakin baya, Ahmed Musa ya jagoranci ƙulla yarjejeniya da RFI Hausa, wadda ya ce ita ce irinta ta farko da ƙungiyar ta taɓa samu tun kafuwarta. Yarjejeniyar ta kunshi samar da kayan wasanni da kuma kayayyakin aikin sada zumunta (Social Media), wanda zai ƙara inganta ayyukan ƙungiyar da kuma hulɗarta da duniya ta zamani.

Musa ya ce kasancewarsa a matsayin Manajan ƙungiyar ba zai hana shi taka leda ba idan buƙatar hakan ta taso. Ya bayyana cewa duk lokacin da ya ke wajen aiki, Ciyaman na ƙungiyar zai ci gaba da kula da duk wasu al’amuran ofishin ba tare da tangarɗa ba. Wannan, a cewarsa, zai tabbatar da cewa shugabancin ƙungiyar bai tsaya ga mutum ɗaya ba.

A ƙarshe, Ahmed Musa ya buƙaci gwamnatin jihar Kano da ta ƙara zage damtse wajen tallafa wa ƙungiyar da kayan aiki da kuɗi. Ya ce burinsu shi ne su mayar da Pillars ƙungiyar da za a riƙa tsoro a gasar ƙwallon ƙafa a Nijeriya, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan an samu cikakken tallafi daga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoPillars
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Next Post

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

2 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

3 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

4 days ago
Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa
Wasanni

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

5 days ago
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain
Wasanni

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

5 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

6 days ago
Next Post
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

July 24, 2025
Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

Buƙatar Rijistar Sabbin Jam’iyyu Ta Kai 144 — INEC

July 24, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

July 24, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato

July 24, 2025
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

July 24, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

July 24, 2025
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

July 24, 2025
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

July 24, 2025
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

July 24, 2025
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

July 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.