ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Fararen hula

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

“Mun kasance muna jiran a ba mu garin alkama, saboda muna jin yunwa sosai, muna neman abin sha da abinci, kwatsam tankokin sojan Isra’ila suka zo suka kewaye mu, suka fara harba bindiga a kanmu, ba mu iya motsawa ba. Ba mu samu gari ba, an kuma kewaye mu na tsawon sa’a daya da rabi zuwa biyu, wasu sun gudu, wasu an kashe su, wasu kuma sun ji raunuka.” In ji wani dan Gaza game da abin da ya faru gare shi a ranar 21 ga wata.

Tsawon kwanaki 140 ke nan da Isra’ila ta rufe hanyoyin shiga Gaza. A halin yanzu, kashi 93% na iyalai a Gaza ba su da ruwan sha, kuma fiye da kashi 87% na yankunan Gaza sun zama yankunan soja ko kuma sassan da mazauna wurin suka bar muhallansu, kusan mutane miliyan 2.1 aka tilasta musu shiga wani karamin yanki, ba su da abubuwan da ake bukata na yau da kullum. Isra’ila ta hana shigar da kayayyakin agaji, da garin madarar jarirai da man fetur, wanda ya sa abinci da magunguna suka kusan kare a Gaza. Fararen hula na Gaza da dama da suka je wuraren rarraba kayayyakin agaji na Isra’ila da ake kira “Gaza Humanitarian Foundation” (GHF) sojojin Isra’ila ne suka harbe su. Firaministan Falasdinu Muhammad Mustafa ya ce adadin wadanda aka kashe ya wuce 995. A Gaza, Isra’ila tana amfani da yunwa a matsayin makami, har ma wuraren rarraba abinci sun zama “tarkon mutuwa”, mutanen Gaza ba su samu gari ba, a maimakon haka ana kashe su da harbin bindiga.

A ranar 21, kakakin harkokin wajen kasar Sin ya jaddada cewa bai kamata a rika kai wa fararen hula hari ba, kuma bai kamata masu ba da agaji na kasa da kasa su fuskanci barazanar tsaro ba. Bugu da kari, kwanan nan kasashe 25 sun fitar da sanarwar hadin gwiwa suna bukatar a kawo karshen yakin yankin Gaza nan take, tare da bukatar Isra’ila ta bi dokokin kasa da kasa na jin kai, da kuma soke takunkumin da aka sanya na shigar da kayayyakin agaji.

ADVERTISEMENT

Da fatan gwamnatin Isra’ila za ta saurari kiran kasa da kasa na kada ta yi amfani da “yunwa a matsayin makami”. Da kuma gaggauta dakatar da yakin nan take a yankin Gaza, don ba da damar shigar da kayayyakin agaji cikin sauki, tare da tabbatar da hakkin fararen hula.(Mai zane da rubutu: MINA)

Fararen hula
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  
Fararen hula
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
  • Sulaiman
    Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

MASU ALAKA

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”
Ra'ayi Riga

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?
Ra'ayi Riga

Binciken Pew: Me Ya Sa Sin Ta Fi Amurka Samun Anincewar Jama’a?

July 20, 2026
Next Post
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.