ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Fararen hula

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

“Mun kasance muna jiran a ba mu garin alkama, saboda muna jin yunwa sosai, muna neman abin sha da abinci, kwatsam tankokin sojan Isra’ila suka zo suka kewaye mu, suka fara harba bindiga a kanmu, ba mu iya motsawa ba. Ba mu samu gari ba, an kuma kewaye mu na tsawon sa’a daya da rabi zuwa biyu, wasu sun gudu, wasu an kashe su, wasu kuma sun ji raunuka.” In ji wani dan Gaza game da abin da ya faru gare shi a ranar 21 ga wata.

Tsawon kwanaki 140 ke nan da Isra’ila ta rufe hanyoyin shiga Gaza. A halin yanzu, kashi 93% na iyalai a Gaza ba su da ruwan sha, kuma fiye da kashi 87% na yankunan Gaza sun zama yankunan soja ko kuma sassan da mazauna wurin suka bar muhallansu, kusan mutane miliyan 2.1 aka tilasta musu shiga wani karamin yanki, ba su da abubuwan da ake bukata na yau da kullum. Isra’ila ta hana shigar da kayayyakin agaji, da garin madarar jarirai da man fetur, wanda ya sa abinci da magunguna suka kusan kare a Gaza. Fararen hula na Gaza da dama da suka je wuraren rarraba kayayyakin agaji na Isra’ila da ake kira “Gaza Humanitarian Foundation” (GHF) sojojin Isra’ila ne suka harbe su. Firaministan Falasdinu Muhammad Mustafa ya ce adadin wadanda aka kashe ya wuce 995. A Gaza, Isra’ila tana amfani da yunwa a matsayin makami, har ma wuraren rarraba abinci sun zama “tarkon mutuwa”, mutanen Gaza ba su samu gari ba, a maimakon haka ana kashe su da harbin bindiga.

A ranar 21, kakakin harkokin wajen kasar Sin ya jaddada cewa bai kamata a rika kai wa fararen hula hari ba, kuma bai kamata masu ba da agaji na kasa da kasa su fuskanci barazanar tsaro ba. Bugu da kari, kwanan nan kasashe 25 sun fitar da sanarwar hadin gwiwa suna bukatar a kawo karshen yakin yankin Gaza nan take, tare da bukatar Isra’ila ta bi dokokin kasa da kasa na jin kai, da kuma soke takunkumin da aka sanya na shigar da kayayyakin agaji.

ADVERTISEMENT

Da fatan gwamnatin Isra’ila za ta saurari kiran kasa da kasa na kada ta yi amfani da “yunwa a matsayin makami”. Da kuma gaggauta dakatar da yakin nan take a yankin Gaza, don ba da damar shigar da kayayyakin agaji cikin sauki, tare da tabbatar da hakkin fararen hula.(Mai zane da rubutu: MINA)

Fararen hula
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Halarci Bikin Bude Baje Kolin Sin Da ASEAN Na 23
Fararen hula
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina
  • Sulaiman
    Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an
  • Sulaiman
    Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

MASU ALAKA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka
Ra'ayi Riga

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026
Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Next Post
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina

September 20, 2026
Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina

Pate Ya Jinjina Wa Sauye-sauye Da Inganta Harkokin Lafiya A Katsina

September 20, 2026
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an

September 20, 2026
Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

Ko Kano Pillars Za Su Iya Taka Wa Doma United Burki A Yau?

September 20, 2026
An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

An Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Asiya Karo Na 20 A Nagoya Na Japan

September 20, 2026
Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

Trump Ya Hana CNN Da Wasu Kafofin Yaɗa Labarai Shiga Fadar White House

September 19, 2026
Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

Adadin Tafiye-Tafiyen Da Jiragen Kasa Masu Jigilar Fasinjoji Suka Yi A Sin Ya Kai Matsayin Koli A Watanni 8 Na Bana

September 19, 2026
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Bauchi Ta Yi Allah-wadai Da Kama Masu Kaɗa Ƙuri’a

September 19, 2026
Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

Kungiyar ’Yan Kasuwar Kaduna Ta Rantsar Da Sabon Shugaban Riƙo

September 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Sin Na Fatan Inganta Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

September 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.