• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamntin Jihar Filato Ta Dakile Sayar Da Kwantan Kwan Gidan Gona

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Gwamntin Jihar Filato Ta Dakile Sayar Da Kwantan Kwan Gidan Gona
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihar Filato ta kasance daya daga cikin jihohin da ke a kan gaba wajen masana’antun da ke samar da kwan gidan gona.

Ta kuma kasance a kan gaba wajen samar da sana’oin yi, musamman ganin ana da sama da gidajen da ake yin kiwon Kajin gidan gona 4,000, inda kusan masana’antun da ake yin kiwon Kajin, kida da ma;aikata da suka kai daga 10 zuwa 20.

  • Gobara Ta Kone Dukiyar Miliyan 39 A Kwara

Sai dai, wasu kalubale sun yiwa masana’antun daurin demon minti, inda hakan ya tilasta wasu daga cikin masana’antun dakatar da yin aiki ko kuma daina yin sana’ar baki daya.

Wadanda kuma suka jure ci gaba da yin sana’ar, suna samar da kwan kasa da yadda suke samar wa a baya.

Wasu daga cikin manyan matsalolin sun hada da tsadar abincin su, da magungunna su da rashin samun kasuwa.

Labarai Masu Nasaba

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Bugu da kari, kafin wannan akwai kuma bullar cutar murar tsintsaye wacce ta janyo raguwar kajin na gidan gona, haka hunturun da aka yi a shekarar da ta wuce ya shafi fannin saboda sanyin da aka yi mai tsanani, inda sanyin ke janyo raguwar kwayayen da ya kamata a kyankyashe.

Kari akan wannan kalubalen da kunno kai a yanzu a jihar shine, shirin sauya sabbin kudi dababban bankin Nijeriya ya fito da shi.
Wannan kalubalen ya janyo shugaban kungiyar masu kiwon Kajin reshen jihar Johnson Bagudu ankarar da bankin akan illlar da hakan ya haifar wa da fannin nasu, iinda ya ce, lamarin na ci gaba da kara munana.

Bagudu ya ce, kalubalen ya janyo karyewar farashin kwan wanda a baya ake sayar da kirat kan Naira 2,100 amma a yanzu, ana sayar da shi kan Naira 1,000, inda ya ce wannan ya haifarwa da masu yin asara.

Ya ce, hakan ya janyo kwan ya yi kwantai saboda wasu masu kiwon sun gaza sayar da shi wasu msu sayen sun saya akan bashi wadanda kuma suka siya sun tura kudin ne ta hanyar bakin ba wai gundarin kudin suka biya ba, inda hakan ya kara jefa masu samar da kwan a cikin matsala,inda ya yi kira da gwamnatin jihar da ta kawo masu dauki.

Hakan ya sa gwamnatin jihar ta fitar da sanawa ta hanyar kakakin yada labaran gwamnatin Makut Macham, inda gwamnatin ta saye sauran kwan ta kuma umarci masu kiwon su kais u kai tsaye zuwa ga gidajen marayu, makarantun gwamnati, asibitocin gwamnati don rabar da su kyauta.

Bagudu ya tabbatar da cika wannan umarnin na gwamnatin, inda ya sanar da cewa, bayan da kungiyar ta dauki kididdigar yawan kwan da ‘ya’yan suka samar, nan take suka cika umarnin na gwamtain jihar na tura kwan inda ta bayar da umarnin akai.

Sai dai, shugaban ya sanar cawa, har yanzu suna ci gaba da jiran gwamnatin ta tura masu kudaden na kwan da suka rabar, inda ya kara da cewa, wannan daukakin na gwamnain, ya taimaka masu domin farashin kwan ya fara karuwa a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Sa Ran Kasuwar AI Ta Kasar Sin Za Ta Habaka Ta Kai Sama Da Dala Biliyan 26 A Shekarar 2026

Next Post

Jami’in Afirka Ta Kudu: Jagororin Dukkan Kasashen BRICS Za Su Halarci Taron Kolin BRICS Din Na Bana

Related

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

2 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

3 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

5 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

6 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

14 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

15 hours ago
Next Post
Jami’in Afirka Ta Kudu: Jagororin Dukkan Kasashen BRICS Za Su Halarci Taron Kolin BRICS Din Na Bana

Jami’in Afirka Ta Kudu: Jagororin Dukkan Kasashen BRICS Za Su Halarci Taron Kolin BRICS Din Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.