• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

by Sulaiman Bala Idris
3 years ago
in Bakon Marubuci
0
zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Inji Matawalle, gwamnan Jihar Zamfara. Ya ce, jama’a fa su dau bindiga su kare kansu daga barnar ‘yan bindiga a fadin Jihar.

Ya kamata a kira taron gaggawa na majalisar dinkin duniya, a sanar musu cewa a Nijeriya, kasar da ake karyar giwar Afirka, a Jihar Zamfara inda ‘yan fasa-kauri daga kasashen duniya suke satar ma’adinai – gwamna ya bada umurnin talakawansa su dau bindiga.

  • Idan Aka Samu Wanda Ya Fi Ni Cancantar Zama Wanda Zai Yi Wa Tinubu Mataimaki Zan Janye —Masari

A gabadaya kananan hukumomi 14 na Zamfara babu karamar hukuma guda daya da babu barnar ‘yan binidga, hatta a babban birnin jihar, wato Gusau, kana yin kasake kaman gaula, za a sace ka, babu ruwansu su ‘yan bindigan.

Kafin a fara sata da fasa kaurin ma’adinai a Jihar Zamfara, babban abin da al’ummar Jihar suna tinkaho da takama ne da noma, ma’ana da shi suke yin arziki har su iya hada kafada da sauran attijiran Nijeriya, su yi aure, su gina gidajen alfarma, su je Hajji, su yi layya, su yi tuwo da miyar sallah. Bayan attijarai da suke kasuwanci da noma, sauran al’umma wato talakawa da noma suka dogara don shuka abin da za su ci na tsawon shekara. Wanda ya yi saura kuma su sayar don samun ‘yan canjin biyan kananan bukatu.

Mu koma kan umurnin Gwamna Matawalle na cewa kowa ya dau bindiga. Duk da a bayyane yake ga kowa, amma yana da kyau karin bayani. Ta ya mutanen da suke gudun hijira za su iya daukar bindiga? Ta ina mutanen da aka hana zuwa gonakinsu za su iya daukar bindiga?
Da farko dai wannan bindigar ba a bishiya ake tsinkota ba. Sayar da ita ake a kasuwa, da tsada ma. Mutumin da zai iya mallakar bindiga ta halastacciyar hanya, dole ya zama ya fi karfin abin da zai ci. Da yawan mutanen sun galabaita, ta kansu suke. Da yawa an yi musu koren kare daga kauyukansu, babu muhalli ballantana gonar shuka.
Gwamna Matawalle duk bai yi la’akari da irin wadannan abubuwa ba, na halin kuncin da mafi yawa ke ciki. Wanda zai hana musu ikon mallakar bindigar da ya bada umurnin su dauka don samarwa kansu da kariya. Tunda gwamnatin tarayya da ta Jiha ta gaza.

Labarai Masu Nasaba

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Akwai abubuwa masu ban tsoro sosai ga wannan sanarwar, kuma dukkan abubuwan sun shafi al’umma ne kaitsaye, sun shafi zamantakewa, tsaro da zaman lafiya.
Na farko, yana nufin kaitsaye babu wani tantama cewa gwamnati ta gaza, kuma babu wani abu da za ta iya yi wurin samar da tsaron rayuka da dukiyar al’ummar Jihar Zamfara, wanda shi ne ginshikiin zamanta hukuma mai cikakken iko. Halastaccen iko shi ne yake bambanta hukuma irin ta Zamfara da hukuma irin ta su dan iskan gari, Turji. Wannan halascin kuwa ya gangaro ne tun daga zabe (halastaccen zabe ne ko magudi) zuwa rantsar da gwamna. Yana nufin akwai wani tsari da aka biyo ta cikinshi wurin samar da gwamnatin. Duk wannan tsarin, ana kiyaye shi ne saboda ita gwamnatin ta kare rayuka da dukiya.

Na biyu, idan makamai suka fara yawo barkatai a cikin jihar Zamfara, za a sha mamaki. Saboda halin kuncin da mutane suka tsinci kansu, ga matsiyacin talauci, babu noma babu aiki. Ita kuma yunwa ba a iya yi mata kawaici, ko da kuwa ana son yi. Mutumin da ke jin yunwa cikin matsanancin kuncin rayuwa, yana iya aikata komi don samun mafita. Akwai mamaki a ce gabadaya masana harkar tsaro da zamantakewar rayuwa da ke tare da Gwamna Matawalle sun kasa fahimtar wannan. Ko don, ba mu sani ba, watakil sun nuna mishi rashin gamsuwa, amma ya cije, tunda gwamna ne.

Yadda ake harkallar satar ma’adanai a Zamfara, idan ya zama kowa na da lasisin daukar bindiga, abin ba zai yi kyau ba. Saboda za a koma rige-rigen kama filayen hako ma’adinai ne, wanda zai sa a rika farmakar juna a tsakanin iyayen daba. Wannan kuma ba yana nufin za a samu zaman lafiya ba ne a Jihar Zamfara, saboda gabadaya rikicin akan dukiya ne ake yin shi. Daga satar Shanu zuwa satar mutane, zuwa satar duk abin da zai yiwu a sata.

Mutane na iya samarwa kansu mafita wurin kare yankunansu ta hanyar yin kwamitin tsaro a matakin unguwanni da sauransu. Wannan zai taimaka musu idan za su ma mallaki bindigar ne, za su yi haka cikin tsarin da duk ranar da wani bako ya zo da mugun nufi za su iya fahimtarshi da manufarsa.

Su kuma wadanda aka tarwatsa daga yankunansu suke gudun hijira a wurare mabambanta, Allah Ya samar musu da mafita ta inda ba su tsammani. Tashin hankalin ya wuce misali, tunda har gwamnati ta gaza, ta ce kowa ya kare kansa. Ko ta ina me harbi ka ruga zai iya fuskantar mai dauke da bindigar da ke sarrafa kanta?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Ceto Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Boko Haram Suka Sace, Ruth Bitrus, A Borno

Next Post

Mane Ya Zama Dan Wasa Na 10 A Buga Wa Bayern Munchen Wasa

Related

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
Bakon Marubuci

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

2 weeks ago
Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

3 weeks ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

1 month ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

2 months ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

2 months ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

3 months ago
Next Post
mane

Mane Ya Zama Dan Wasa Na 10 A Buga Wa Bayern Munchen Wasa

LABARAI MASU NASABA

Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Wutar lantarki

Arewa Maso Gabas Ce Za Ta Biya Kudin Wuta Mafi Tsada A Sabon Tsarin Lantarki

July 25, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

July 25, 2025
Manzon Allah

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

July 25, 2025
‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli

‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli

July 25, 2025
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.