• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Dau Bindiga: Babu Hukuma A Zamfara?

by Sulaiman Bala Idris
3 years ago
in Bakon Marubuci
0
zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Inji Matawalle, gwamnan Jihar Zamfara. Ya ce, jama’a fa su dau bindiga su kare kansu daga barnar ‘yan bindiga a fadin Jihar.

Ya kamata a kira taron gaggawa na majalisar dinkin duniya, a sanar musu cewa a Nijeriya, kasar da ake karyar giwar Afirka, a Jihar Zamfara inda ‘yan fasa-kauri daga kasashen duniya suke satar ma’adinai – gwamna ya bada umurnin talakawansa su dau bindiga.

  • Idan Aka Samu Wanda Ya Fi Ni Cancantar Zama Wanda Zai Yi Wa Tinubu Mataimaki Zan Janye —Masari

A gabadaya kananan hukumomi 14 na Zamfara babu karamar hukuma guda daya da babu barnar ‘yan binidga, hatta a babban birnin jihar, wato Gusau, kana yin kasake kaman gaula, za a sace ka, babu ruwansu su ‘yan bindigan.

Kafin a fara sata da fasa kaurin ma’adinai a Jihar Zamfara, babban abin da al’ummar Jihar suna tinkaho da takama ne da noma, ma’ana da shi suke yin arziki har su iya hada kafada da sauran attijiran Nijeriya, su yi aure, su gina gidajen alfarma, su je Hajji, su yi layya, su yi tuwo da miyar sallah. Bayan attijarai da suke kasuwanci da noma, sauran al’umma wato talakawa da noma suka dogara don shuka abin da za su ci na tsawon shekara. Wanda ya yi saura kuma su sayar don samun ‘yan canjin biyan kananan bukatu.

Mu koma kan umurnin Gwamna Matawalle na cewa kowa ya dau bindiga. Duk da a bayyane yake ga kowa, amma yana da kyau karin bayani. Ta ya mutanen da suke gudun hijira za su iya daukar bindiga? Ta ina mutanen da aka hana zuwa gonakinsu za su iya daukar bindiga?
Da farko dai wannan bindigar ba a bishiya ake tsinkota ba. Sayar da ita ake a kasuwa, da tsada ma. Mutumin da zai iya mallakar bindiga ta halastacciyar hanya, dole ya zama ya fi karfin abin da zai ci. Da yawan mutanen sun galabaita, ta kansu suke. Da yawa an yi musu koren kare daga kauyukansu, babu muhalli ballantana gonar shuka.
Gwamna Matawalle duk bai yi la’akari da irin wadannan abubuwa ba, na halin kuncin da mafi yawa ke ciki. Wanda zai hana musu ikon mallakar bindigar da ya bada umurnin su dauka don samarwa kansu da kariya. Tunda gwamnatin tarayya da ta Jiha ta gaza.

Labarai Masu Nasaba

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

Akwai abubuwa masu ban tsoro sosai ga wannan sanarwar, kuma dukkan abubuwan sun shafi al’umma ne kaitsaye, sun shafi zamantakewa, tsaro da zaman lafiya.
Na farko, yana nufin kaitsaye babu wani tantama cewa gwamnati ta gaza, kuma babu wani abu da za ta iya yi wurin samar da tsaron rayuka da dukiyar al’ummar Jihar Zamfara, wanda shi ne ginshikiin zamanta hukuma mai cikakken iko. Halastaccen iko shi ne yake bambanta hukuma irin ta Zamfara da hukuma irin ta su dan iskan gari, Turji. Wannan halascin kuwa ya gangaro ne tun daga zabe (halastaccen zabe ne ko magudi) zuwa rantsar da gwamna. Yana nufin akwai wani tsari da aka biyo ta cikinshi wurin samar da gwamnatin. Duk wannan tsarin, ana kiyaye shi ne saboda ita gwamnatin ta kare rayuka da dukiya.

Na biyu, idan makamai suka fara yawo barkatai a cikin jihar Zamfara, za a sha mamaki. Saboda halin kuncin da mutane suka tsinci kansu, ga matsiyacin talauci, babu noma babu aiki. Ita kuma yunwa ba a iya yi mata kawaici, ko da kuwa ana son yi. Mutumin da ke jin yunwa cikin matsanancin kuncin rayuwa, yana iya aikata komi don samun mafita. Akwai mamaki a ce gabadaya masana harkar tsaro da zamantakewar rayuwa da ke tare da Gwamna Matawalle sun kasa fahimtar wannan. Ko don, ba mu sani ba, watakil sun nuna mishi rashin gamsuwa, amma ya cije, tunda gwamna ne.

Yadda ake harkallar satar ma’adanai a Zamfara, idan ya zama kowa na da lasisin daukar bindiga, abin ba zai yi kyau ba. Saboda za a koma rige-rigen kama filayen hako ma’adinai ne, wanda zai sa a rika farmakar juna a tsakanin iyayen daba. Wannan kuma ba yana nufin za a samu zaman lafiya ba ne a Jihar Zamfara, saboda gabadaya rikicin akan dukiya ne ake yin shi. Daga satar Shanu zuwa satar mutane, zuwa satar duk abin da zai yiwu a sata.

Mutane na iya samarwa kansu mafita wurin kare yankunansu ta hanyar yin kwamitin tsaro a matakin unguwanni da sauransu. Wannan zai taimaka musu idan za su ma mallaki bindigar ne, za su yi haka cikin tsarin da duk ranar da wani bako ya zo da mugun nufi za su iya fahimtarshi da manufarsa.

Su kuma wadanda aka tarwatsa daga yankunansu suke gudun hijira a wurare mabambanta, Allah Ya samar musu da mafita ta inda ba su tsammani. Tashin hankalin ya wuce misali, tunda har gwamnati ta gaza, ta ce kowa ya kare kansa. Ko ta ina me harbi ka ruga zai iya fuskantar mai dauke da bindigar da ke sarrafa kanta?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Ceto Wata ‘Yar Makarantar Chibok Da Boko Haram Suka Sace, Ruth Bitrus, A Borno

Next Post

Mane Ya Zama Dan Wasa Na 10 A Buga Wa Bayern Munchen Wasa

Related

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

3 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

1 month ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

1 month ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

3 months ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

3 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

3 months ago
Next Post
mane

Mane Ya Zama Dan Wasa Na 10 A Buga Wa Bayern Munchen Wasa

LABARAI MASU NASABA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

July 4, 2025
NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

July 4, 2025
Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.