• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

by Leadership Hausa
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau kimanin wata daya ke nan, da mummunan ambaliyar ruwan sama ta auka ma wasu sassan garin Maiduguri, babban birnin Jihar Borno,abinda yayi sanadiyar lalacewar kayan al’umma na miliyoyin Naira tare da mutuwar mutane da dama.

Annobar ta kuma yi awon gaba da daruruwan gonaki da lalata gidaje da dama, da wasu wuraren da ake gudanar da hada-hadar kasuwanci da dai sauransu.

  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin
  • Gwamna Lawal Ya Ba Da Kyautar Mota Ga Ƙungiyar Tsaffin Manyan Sakatarorin Da Suka Yi Ritaya A Zamfara

Wasu kwararru sun danganta annobar, a matsayin wadda ta fi mafi muni a cikin shekara 30 da suka wuce, duba da yadda tun da farko, aka kiyasta ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 30.

Sai dai kuma, wasu rahotanni da ba a tabbatar da sahihancinsu ba a hukumance, sun ayyana adadin wadanda suka rasu da cewa sun zarce hakan.

Annobar ta shafi sama da miliyoyin mutane, wadda kuma aka samu labarin, ta raba mutane 414,000 daga matsagunan su.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Tun bayan aukuwar iftibla’in kungiyoyi na kasashen waje, gwamnatin tarayya, gwamnatin jihohi, manyan fitattu ‘yan Nijeriya da sauran wasu kamfanoni, suka bai wa gwamnatin Jihar Borno gudunmawar kudade da wasu kayan agaji, bisa nufin tallafa wa wadanda iftibla’in ya aukawa.

Wannan gudunmawar tasu, domin a taimaka wa wadanda iftibla’in ya shafa, abin yabawa ne.

Gwamnatocin tarayya da na jihohi sun dauki matakan gaggawa domin agazawa wadanda lamarin ya shafa, musamman ma idan aka yi la’akari da yadda wadannan al’umomin suke ci gaba da jurewa jimirin kalubalen ayyukan ‘yan ta’adda da kuma na, ‘yan bindiga daji.

Gwamnatin jihar, ta kafa kwamitin, da zai yi nazarin iftibla’in wanda kuma zai ba gwamnatin shawara, a kan yadda za a yi gaggawar sake mayar da wadanda lamarin ya shafa, zuwa ga matsugunan su don ci gaba da rayuwa.

Tuni dai, gwamnatin ta samu gudunmawar kudi na Naira biliyan 7 daga cikin alkawuran da wasu masu taimakawa suka yi na bayar da ta su gudunmawar.

Wannan jaridar ta jinjina wa wadanda suka bada gudunmawar daga kungiyoyi na waje, da na cikin gida a kan tallafawa al’umomin da iftibla’in ya shafa.

Sai dai kuma, duk da irin wannan gudunmawar da suka bayar, tallafin bai isa ga wadanda lamarin ya shafa ba.

Idan aka yi la’akari da yadda aka samu raguwar ruwan sama, ya kamata mahukunta su gaggauta samar da tsarin sake mayar da wadanda lamarin ya shafa, zuwa ga matsugunan su.

A ra’ayinmu, aikin da ke gaba na bukatar yin kokari tare da samun hada kai.

Naira biliyan 7 da aka samu ta gudanmawar da aka bayar, da kuma sauran alkawuran kudi da aka yi, sun kai jimillar Naira biliyan 13, a saboda haka, ya zama wajibi ne a tattara wadannan kudaden yadda ya dace, domin sake gyaran matsugunan al’umomin da abin ya shafa.

A yayin da muke yin wannan rokon, muna kuma yin kira da ayi gyara yadda al’amuran ke tafiya a sansan da gwamnatin jihar ta bude a jihar, domin ajiye al’umomin da abin ya shafa, musamman ma yadda ake ganin ana sayar da wasu kayan da aka bayar domin taimakawa ‘yan gudun hijirar na ambaliyar ruwan.

Akwai babban nauyi a kan hukumomi na kare wadanda lamarin ya shafa, daga batagarin jami’an gwamnati, masu cin hanci, ta hanyar yin amfani da bazar wadanda ifitibla’in ya shafa.

A bangare daya kuma, gudunmawar kudaden da aka samu, ya zama wajibi ne, a yi amfani da su yadda ya dace, musamman domin wadanda abin ya shafa, su sake tsayawa da kafafunsu su kuma ci gaba da wata sabuwar rayuwa.

Kazalika ma, ta hannu daya kuma, muna yin kira ga wadanda suka yi alkawarin bayar da gudunmawar su ta kudi, da su cika alkwarinsu a kan lokaci, wanda hakan, zai ragewa wadanda iftibila’in ya shafa na radadin rayuwa.

A namu ra’ayin, shi ne sake giggina matsugunan al’ummomin da lamarin ya shafa don su koma su ci gaba da gudanar da kasuwancin su.

Wadannan matakan, na bukatar daukar inganttaun matakai na gajere da na dogon zango, duba da yadda al’ummomin da abin ya shafa sun zama tamkar sai sun sake wani sabon lale, na ci gaba da rayuwa, muna kuma kira, da a samar da shirin sake gina gidaje na wadanda suka rasa gidajen su, saboda iftibla’in.

Mun gamsu kokarin da gwamnatin Borno yake yi na taimakawa, bama kamar idan aka yi la’akari da tuni, ta fara yin abin da ya dace.

Muna bayar da shawarar cewa, ya kamata a hada wannan kokarin da ake yi, tare da bayar da tallafin yin sana’oin kasuwanci ga wadanda abin ya shafa.

Kazalika, kar a bar manoman da amfanin gonakan su ya lalace sanadiyar amlabiyar, domin suma suna da bukatar tallafa masu da Iri da sauran kayan aikin gona domin su sake komawa yin sana’arsu, ta noma.

Ya kamata, a samar da shirin gaggawa da kuma wanzar da shi, a kan lokaci, musamman ma domin sake gyaran kayan da suka lalace, ciki har da hanyoyi da sauransu.

Bisa bayanan da aka samu, shekarun da suka wuce, irin wadannan al’ummomin da ifibla’in ya shafa, ba sa samun kulawar da ta kamata.

A saboda irin wannan muna gargadin hukumomin bayar da agajin gaggawa kamar irinsu NEMA, a kan samar da daukin jeka na yi ka, wato kawai, kamar yadda suka saba yi, na rabar da Katifu, kwanukan rufi, ga wadanda wata annobar daban ta aukawa.

Maimakon hakan, ya kamata NEMA da gwamnati Borno, su hada karfi da karfe don samar da kwakkwaran shirin sake gina matsugunan alu’mmomin da abin ya shafa.

Nuna damuwar da kungiyoyin kasashen waje suka yi ga wadanda ifibla’in ya shafa, abin yabawa ne, muna kuma kira da a kara yawan fahimta.

Aikin sake mayar da al’ummomin jihar Borno,da iftibla’in ya shafa, na bukatar daukar matakan gaggawa da kuma yin amfani da kudaden da aka bayar na gudunmawa yadda ya dace.

Daukacin abin da ake bukata a yanzu shi ne, mayar da hankali a kan kalubalen tare da tabbatar da cewa, al’ummomin da iftibla’in ya shafa, gudunmawar ta isa gare su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmbaliyaIftila'iMaiduguriRuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya

Next Post

Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

7 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

8 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

16 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

21 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

24 hours ago
Next Post
Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.