• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A KUSKURA: Yadda Kayan Maye Ya Zama Ruwan Dare A Tsakanin Al’umma

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
A KUSKURA: Yadda Kayan Maye Ya Zama Ruwan Dare A Tsakanin Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, an yi ta samun yaduwar wani kayan maye mai hatsarin gaske wanda aka fi sani da A kuskura/Kuskura ko Akurkura, wanda ake yin shi da Tumfafiya hade da ganyen wiwi da na ‘tobacco’ da wasu sinadarai, wanda kuma ya fi yaduwa a yankin arewaci da kudu maso yammacin Nijeriya. Wasu lokutan, Akuskura yana kai mutum ga gargarar mutuwa saboda tsananin karfin sinadaran da aka hada shi da su.

Sunan Akuskura, wanda a wasu lokuta ake kira kuskura ko akurkura, ya samo asali ne daga kalmar “kuskura” na Hausa. Ana amfani da sinadarin Akuskura ne ta hanyar kuskure baki a tofar, ko kuma a shaka a hanci. Da zarar an yi hakan, nan take yake fara aikin sa, inda yake gusar da hankali kai tsaye a mafi yawancin lokuta, da kuma kara kuzarin gabobin jiki, rudar da tunani da hana bacci. A wasu lokutan kuma yakan saka mutum ya shiga cikin mawuyacin hali na tsananin kishi da rikewar makogoro ko suma.

  • Hukumar NDLEA Ta Cafke Wani Basarake Da Miyagun Kwayoyi A Jihar Sakkwato
  • NDLEA Ta Yi Nasarar Cafke Shahararren Dan Kasuwar Miyagun Kwayoyi Ta Yanar Gizo A Abuja

A kwanan hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, ta kama sama da kwalabe dubu bakwai na haramtacciyar sinadarin a hanyar Abuja zuwa Kaduna, wadda aka aika su zuwa jihohin Borno, Kano, Kaduna, Sokoto, Zamfara, Gombe da Nasarawa. Duk da cewa wannan shi ne mafi girman kamu da akayi na sinadarin da akayi, akwai da dama da aka kama a wurare mabanbanta kafin shi.

Biyo bayan kamen da aka yi, babban daraktan hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa, NAFDAC, a wata ganawa da manema labarai a hedikwatar hukumar dake Abuja a ranar 19 ga watan Agusta, ta sanar da hana amfani da sinadarin a hukumance. Ta ce hukumar ta samu rahotanni da dama na amfani da Kurkura musamman a yankin Kudu maso Yamma da Arewacin kasar nan. Daraktan ta kara da cewa ganin hakan ne ya sa hukumar ta shirya taron manema labarai don kara tabbatar wa al’umma haramcin amfani da sinadarin kuskura, sakamakon illolin da take dauke da su.

Akuskura nau’in miyagun kwayoyi ne da ake kira sabbin sinadaran gusar da hankali, a turance (New Psychoactive Substance). NPS sinadarai ne wadanda yarjejeniyar 1961 akan kayan shaye-shaye da Yarjejeniyar 1971 na majalisar dinkin duniya basu ambace su a matsayin kayan shaye-shaye ba saboda a lokacin babu bullar su. Sai dai duk da cewa basa cikin jerin kwayoyi na wadannan yarjejeniya, NPS suna iya daukan illoli ga lafiyar jiki masu tasirin gaske. Wannan yana nuna cewa akuskura ya shiga nau’in miyagun kwayoyi, kamar yanda hukumar NAFDAC ta ayyana

Labarai Masu Nasaba

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

Duk da cewa yana da illoli ga lafiyar dan Adam, kuma yana dauke da sinadaran maye da suka hada da wiwi da sauran su, Akuskura yana yawo a tsakanin masu sayar da maganin gargajiya a garuruwa daban-daban, musamman ma a cikin arewacin Nijeriya a matsayin magani, wanda kuma bincike ya tabbatar da cewa baragurbin kwaya ne.

Masu sayar da shi sukan yi ikirarin cewa yana maganin sanyi, mura, tari, ciwon kai, hawan jini, ciwon suga, karin kuzarin mazantaka, maganin amosani, maganin gajiya da dai sauran su.

A zahirin gaskiya, babu wani ingantaccen nazari da masana sukayi wanda suka samu yakinin cewa Akuskura na maganin ko da daya ne daga cikin wadannan cututtuka. Abun da bincike ya tabbatar shine; kuskura sinadari ne na kwaya wanda hukuma ta haramta amfani da shi.

Wannan kuwa yana nuna cewa duk mai sayar da Kuskura yana taka doka ne kuma zai iya gamuwa da fushin hukuma, haka ma wanda ya ke sha, da wanda yake safarar su, kamar yanda shugaban hukumar NDLEA, Burgediya Janar Mohamed Buba Marwa ya ayyana a wani hira da yayi da gidan radiyon BBC Hausa, inda yace hukumar NDLEA ba zata saurarawa masu ta’amuli da sinadarin Akuskura ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mace Za Ta Iya Yin Limancin Sallah?

Next Post

Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra

Related

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

2 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

3 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

3 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

4 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

6 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

7 hours ago
Next Post
Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra

Ya Kashe Yayansa Kan Kudin Wutar Lantarki Naira 1,500 A Anambra

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.