• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla ‘yan Nijeriya 78 ne suka rasa rayukansu, yayin aka yi garkuwa da mutum 12 a fadin Nijeriya tun lokacin da Shugaban kasa Tinubu ya sha rantsuwar fara aiki.

Lamarin ya faru ne a jihohin Ribas, Zamfara, Kaduna, Ogun, Sakkwato da kuma Babban Birnin Tarayya.

  • Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Bindiga 4, Sun Kwato Makamai A Jihar Zamfara

An samu wannan bincike ne daga masu bindiddigin sha’anin tsaron Nijeriya da ke da alaka da kasashen ketare.

Rahoton ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun halaka mutum hudu da kuma bille wa mutum biyu kawuna a Jihar Ribas a ranar 29 ga Mayu.

A ranar 30 ga Mayu kuwa, ‘yan bindiga sun kashe shugaban kungiyar sa-kai tare da wasu mutum 24 a Jihar Zamfara. Haka kuma a wannan rana ta 30 ga Mayu, an yi garkuwa da shugabannin matan jam’iyyar APC bayan sun halarci bikin rantsar da gwamnan Jihar Kaduna.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A dai wannan rana, ‘yan bindiga sun kasha wani mutum tare da yin garkuwa da matarsa da ‘ya’yansa guda hudu a Jihar Kaduna. Sannan kuma a wannan rana ta 30, wasu da ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne sun halaka mutum shida a Jihar Ribas.

A ranar 31 ga Mayu, ‘yan bindiga dadi sun kai hari a wata gona da ke Jihar Ogun, inda suka kashe mutum uku tare da yin garkuwa da mutum biyu. A Abuja kuwa, ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutum hudu a ranar 4 ga Yunin 2023.

‘Yan Nijeriya suna cikin damuwa na ganin an yi musu maganin babbar matsalar da ta addabesu na kisan gilla da ake musu babu dare babu rana, wanda hakan ya janyo asarar yaruka da dama da kuma dimbin dukiyoyi sakamakon rashin tsaro. Ko Tinubu zai iya cimma burinsa wajen kawo karshen rashin tsaro a Nijeriya?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

Next Post

Wakilin Sin A Taron Vienna Ya Soki Lamirin Yarjejeniyar AUKUS

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

4 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

4 weeks ago
Next Post
Wakilin Sin A Taron Vienna Ya Soki Lamirin Yarjejeniyar AUKUS

Wakilin Sin A Taron Vienna Ya Soki Lamirin Yarjejeniyar AUKUS

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

May 22, 2025
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

May 22, 2025
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

May 22, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Tiriliyan 1.5 Don Magance Matsalar Abinci — Minista

May 22, 2025
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur

May 22, 2025
Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

May 22, 2025
Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

Tsaro Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Atiku

May 22, 2025
Ma’aikatan Wutar Lantarki A Katsina Sun Tsunduma Yajin Aiki

Ma’aikatan Wutar Lantarki A Katsina Sun Tsunduma Yajin Aiki

May 22, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 5 Hukuncin Ɗaurin Wata 1 Saboda Awakinsu Sun Cinye Bishiyar Gwamnati A Kano

May 22, 2025
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.