• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sansanin ‘Yan Hijira Na Jibiya: Mutum 15 Sun Mutu, An Haifi 35, Akalla Yara 3,000 Ba Su Karatu

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Hijira

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

Kimanin mutum 15 ne suka rasu kuma mafiyawancinsu mata, da haihuwar jarirai akalla 35 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Jibiya a Jihar Katsina, a cikin watanni uku da suka gabata.

Shugaban ‘yan gudun hijira Malam Sa’adu Salisu ne ya bayyana haka ga manema labarai a lokacin da tawagar ‘yan jarida masu aikawa da rahotanni daga jihar Katsina suka kai ziyarar gani da ido a sansanin da ke makarantar ‘yan mata ta jibiya.

  • Ayyukan’Yan Bindiga: An Rufe Makarantun Gwamnati 19 A Katsina 

Ya kara da cewa sun kai kimanin su dubu 16 da suka fito daga bangarori daban-daban da suka hada da Tsabu, Farfaru, Kwari da Garin Alhaji da Zango da Shinfida da sauran garuruwa da ke kusa da garin Jibiya.
Wadannan mutane dai sun rasa muhallansu ne sakamakon haren-haren ‘yan bindiga da masu satar jama’a domin neman kudin fansa kuma lamarin ya ki ci ya ki cinyewa.
Shugaban ‘yan gudun hijirar ya ce wasu daga cikin ‘yan gudun hijirar basa kwana a sansanin sakamakon rashin wurin kwana mai kyau da rashin gidan sauro da lantarki da ruwan sha da sauran kayayyakin more rayuwa.
“Sannan muna fuskantar matsalar tsaro a wannan wuri, duk wannan yawan namu dan sanda biyu ne kawai ke tare da mu, sannan yanayin da muke ciki abin ba dadin ji musamman matsalar rashin abinci wadatacce.” In ji shi.
Haka kuma Malam Sa’adu Salisu ya kara da cewa lokacin baya suna samun abinci har sau uku a rana amma a hankali a hankali yanzu wani lokaci sau daya suke cin abinci. Ya kara da cewa wasu mutanen ma a kasa suke kwana saboda rashin isassun abin shinfida wasu kuma suna shinfida zannuwansu suna kwana a kai.
Game da matsalar rashin lafiya kuwa shugaban ‘yan gudun hijira ya ce suna samun gudunmawar magunguna daga gwamnati da kungiyoyi da ‘yan siyasa da masu hannu da shuni
A cewarsa yanzu babban abin da ya fi damunsu shi ne yadda yaransu musamman mata kanana fiye da dubu uku ba sa zuwa makaranta saboda halin da suka tsinci kansu a cikin, inda ya ce lallai wannan matsala da ita suke kwana da ita suke tashi.
Da aka ji ta bakinsa, shugaban karamar hukumar Jibiya Hon. Bishir Sabiu Maitan ya ce duk abin da ‘yan gudun hijira ke bukata bakin gwargwado gwamnatin jihar Katsina na yi ba tare da wata matsala ba.
Hon. Maitan ya ce kullum sai an dafa buhun shinkafa goma sha biyar, kuma ya ce bashi da labarin cewa sau daya ake abinci a sansanin ‘yan gudun hijirar, domin gwamnati sau uku take ba da abinci.
Ya kara da cewa babu wata bukata da suka kai wa Gwamna Masari da bai yi masu ba, “saboda haka gwamnati na bakin kokarinta wajan kyautata wa ‘yan gudun hijira, sai dai ajizanci na Dan’adam ba za a rasa ‘yan kurakurai ba.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra'ayinmu)

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.