• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sansanin ‘Yan Hijira Na Jibiya: Mutum 15 Sun Mutu, An Haifi 35, Akalla Yara 3,000 Ba Su Karatu

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Hijira

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

Kimanin mutum 15 ne suka rasu kuma mafiyawancinsu mata, da haihuwar jarirai akalla 35 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Jibiya a Jihar Katsina, a cikin watanni uku da suka gabata.

Shugaban ‘yan gudun hijira Malam Sa’adu Salisu ne ya bayyana haka ga manema labarai a lokacin da tawagar ‘yan jarida masu aikawa da rahotanni daga jihar Katsina suka kai ziyarar gani da ido a sansanin da ke makarantar ‘yan mata ta jibiya.

  • Ayyukan’Yan Bindiga: An Rufe Makarantun Gwamnati 19 A Katsina 

Ya kara da cewa sun kai kimanin su dubu 16 da suka fito daga bangarori daban-daban da suka hada da Tsabu, Farfaru, Kwari da Garin Alhaji da Zango da Shinfida da sauran garuruwa da ke kusa da garin Jibiya.
Wadannan mutane dai sun rasa muhallansu ne sakamakon haren-haren ‘yan bindiga da masu satar jama’a domin neman kudin fansa kuma lamarin ya ki ci ya ki cinyewa.
Shugaban ‘yan gudun hijirar ya ce wasu daga cikin ‘yan gudun hijirar basa kwana a sansanin sakamakon rashin wurin kwana mai kyau da rashin gidan sauro da lantarki da ruwan sha da sauran kayayyakin more rayuwa.
“Sannan muna fuskantar matsalar tsaro a wannan wuri, duk wannan yawan namu dan sanda biyu ne kawai ke tare da mu, sannan yanayin da muke ciki abin ba dadin ji musamman matsalar rashin abinci wadatacce.” In ji shi.
Haka kuma Malam Sa’adu Salisu ya kara da cewa lokacin baya suna samun abinci har sau uku a rana amma a hankali a hankali yanzu wani lokaci sau daya suke cin abinci. Ya kara da cewa wasu mutanen ma a kasa suke kwana saboda rashin isassun abin shinfida wasu kuma suna shinfida zannuwansu suna kwana a kai.
Game da matsalar rashin lafiya kuwa shugaban ‘yan gudun hijira ya ce suna samun gudunmawar magunguna daga gwamnati da kungiyoyi da ‘yan siyasa da masu hannu da shuni
A cewarsa yanzu babban abin da ya fi damunsu shi ne yadda yaransu musamman mata kanana fiye da dubu uku ba sa zuwa makaranta saboda halin da suka tsinci kansu a cikin, inda ya ce lallai wannan matsala da ita suke kwana da ita suke tashi.
Da aka ji ta bakinsa, shugaban karamar hukumar Jibiya Hon. Bishir Sabiu Maitan ya ce duk abin da ‘yan gudun hijira ke bukata bakin gwargwado gwamnatin jihar Katsina na yi ba tare da wata matsala ba.
Hon. Maitan ya ce kullum sai an dafa buhun shinkafa goma sha biyar, kuma ya ce bashi da labarin cewa sau daya ake abinci a sansanin ‘yan gudun hijirar, domin gwamnati sau uku take ba da abinci.
Ya kara da cewa babu wata bukata da suka kai wa Gwamna Masari da bai yi masu ba, “saboda haka gwamnati na bakin kokarinta wajan kyautata wa ‘yan gudun hijira, sai dai ajizanci na Dan’adam ba za a rasa ‘yan kurakurai ba.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista
Labarai

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra'ayinmu)

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.