ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Sansanin ‘Yan Hijira Na Jibiya: Mutum 15 Sun Mutu, An Haifi 35, Akalla Yara 3,000 Ba Su Karatu

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Hijira

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Kimanin mutum 15 ne suka rasu kuma mafiyawancinsu mata, da haihuwar jarirai akalla 35 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Jibiya a Jihar Katsina, a cikin watanni uku da suka gabata.

Shugaban ‘yan gudun hijira Malam Sa’adu Salisu ne ya bayyana haka ga manema labarai a lokacin da tawagar ‘yan jarida masu aikawa da rahotanni daga jihar Katsina suka kai ziyarar gani da ido a sansanin da ke makarantar ‘yan mata ta jibiya.

  • Ayyukan’Yan Bindiga: An Rufe Makarantun Gwamnati 19 A Katsina 

Ya kara da cewa sun kai kimanin su dubu 16 da suka fito daga bangarori daban-daban da suka hada da Tsabu, Farfaru, Kwari da Garin Alhaji da Zango da Shinfida da sauran garuruwa da ke kusa da garin Jibiya.
Wadannan mutane dai sun rasa muhallansu ne sakamakon haren-haren ‘yan bindiga da masu satar jama’a domin neman kudin fansa kuma lamarin ya ki ci ya ki cinyewa.
Shugaban ‘yan gudun hijirar ya ce wasu daga cikin ‘yan gudun hijirar basa kwana a sansanin sakamakon rashin wurin kwana mai kyau da rashin gidan sauro da lantarki da ruwan sha da sauran kayayyakin more rayuwa.
“Sannan muna fuskantar matsalar tsaro a wannan wuri, duk wannan yawan namu dan sanda biyu ne kawai ke tare da mu, sannan yanayin da muke ciki abin ba dadin ji musamman matsalar rashin abinci wadatacce.” In ji shi.
Haka kuma Malam Sa’adu Salisu ya kara da cewa lokacin baya suna samun abinci har sau uku a rana amma a hankali a hankali yanzu wani lokaci sau daya suke cin abinci. Ya kara da cewa wasu mutanen ma a kasa suke kwana saboda rashin isassun abin shinfida wasu kuma suna shinfida zannuwansu suna kwana a kai.
Game da matsalar rashin lafiya kuwa shugaban ‘yan gudun hijira ya ce suna samun gudunmawar magunguna daga gwamnati da kungiyoyi da ‘yan siyasa da masu hannu da shuni
A cewarsa yanzu babban abin da ya fi damunsu shi ne yadda yaransu musamman mata kanana fiye da dubu uku ba sa zuwa makaranta saboda halin da suka tsinci kansu a cikin, inda ya ce lallai wannan matsala da ita suke kwana da ita suke tashi.
Da aka ji ta bakinsa, shugaban karamar hukumar Jibiya Hon. Bishir Sabiu Maitan ya ce duk abin da ‘yan gudun hijira ke bukata bakin gwargwado gwamnatin jihar Katsina na yi ba tare da wata matsala ba.
Hon. Maitan ya ce kullum sai an dafa buhun shinkafa goma sha biyar, kuma ya ce bashi da labarin cewa sau daya ake abinci a sansanin ‘yan gudun hijirar, domin gwamnati sau uku take ba da abinci.
Ya kara da cewa babu wata bukata da suka kai wa Gwamna Masari da bai yi masu ba, “saboda haka gwamnati na bakin kokarinta wajan kyautata wa ‘yan gudun hijira, sai dai ajizanci na Dan’adam ba za a rasa ‘yan kurakurai ba.” In ji shi.

ADVERTISEMENT
Hijira
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Next Post
Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra'ayinmu)

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.