ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
4 years ago
Nijeriya

Fiye da wani lokaci, rahoton da aka fitar na matsayin jami’o’in Nijeriya a ma’aunin jami’o’i na duniya ya nuna cewa, wannan ne lokaci fiye da wani lokacin da ake bukatar a maida da hankali a kan halin da harkar ilimi ta ciki a kasar nan musamman ilimin jami’a a kasar nan.

Rahoton da Cibiyar ‘Times Higher Education’ ta fitar ya nuna cewa, gwarzuwar jami’a a Nijeriya ita ce, Jami’ar Afe Babalola (ABUAD) da ke Ado-Ekiti, wadda ta yi ta 400 a jerin jami’o’in duniya.

  • 2023: Kwankwaso Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Yi Watsi Da APC Da PDP

Cibiyar ta karbu a fadin duniya saboda sahihancin rahotannin da take fitarwa, cikin abubuwan da take lura dasu wajen yanke hukuncin zabar kwazon jami’a sun hada da abin da ya shafi bangaren karantarwa da bincike da kuma yadda jami’ar ta karbuwa a sassan duniya.

ADVERTISEMENT

Yakamata a fahinci cewa, a shekarar 2022 cibiyar ta nazarci jami’o’i 1, 600 a kasashe 99. Cibiyar ta yi nazarin mukala fiye da Miliyan 108 da kuma kundin bincike da jami’o’i fiye da Miliyan 14.4 ta kuma karbi amsar tambayoyi daga masana fiye da 22,000 a fadin duniya.

Babu wata kasar Afrika data zo cikin jami’o’i na 100 na farko a jerin gwarazan jami’o’i duniya. Gwarzuwar jami’a data fi tsari a Afrika ita ce jami’ar kasar Afirka ta Kudu ‘Unibersity of Cape Town’ inda ta zo ta 183 a duniya. A Nijeriya kuma Jami’ar Ibadan da ta Legas suka zo na 401 da 501.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

A yayin da muke taya Jami’ar ABUAD murnar wannan nasarar, mun lura da cewa, wannan yana nuna irin tsananin yadda harkar ilimi ta tabarbarewar a kasar nan.

Duk da matukar muhimmancinta a wajen tafiyar da tattalin arzikin kasa gwamnatocin da suka gabata sun yi watsi da harkar ilimi, ta hanyar nakasa kasafin kudin da ake tanadar wa bangaren ilimin.

Akwai bukatar a sake nazarin kasafin kudin da jihohin kasar nan 36 ke samar wa bangaren ilimi musamman ma ganin kowacce jiha a halin yanzu ta mallaki jami’a ta kanta. Yayin da hukumar Majalisar Dinkin Duniya ta nemi a ware kashi 25 na kasafin kudin da aka kiyasta kashe ga bangaren ilimi har yanzu Nijeriya bata kai ga samar da kashi 15 ba.

A kasafin kudin shakarar 2022 gwmanatin Nijeriya ta ware wa bangaren ilimi Naira Tiriliyan 1.29 wanda ke nuna cewa kashi 7.9 kenan na kasasfin kudin da aka yi a shekarar. Wannan na nuna cewa an yi wa bangaren ilimi kashi 10 kenan duk kuwa da cewa, Majalisar Dinkin Duniya ta nemi ne aware kashi 25 na kasafin kudin a duk shekara don tallafa wa harkar ilimin al’umma.

Idan za a iya tunawa gwamnatin Buhari ta kasafta kashe Naira Tiriliyan 55.3 don gudanar da harkokin gwamnati a cikin shakara 6 na mulkinta amma Naira Tiriliyan 3.5 kawai aka ware wa bangaren ilimi wanda ke nuna kashin yana kasa da kashi 10, wanda ke nuna karara lamarin ilimi ba abin da gwamnatin ta dauka da muhimmanci bane.

Abin takaici a nan shi ne bangaren ilimi ya yi fama da matsalar kudade ga rashin kayan aiki da kuma karancin albashi ga kuma karancin ma’aikata wanda duk suna taimakawa wajen haifar da matsaloli ga bangaren ilimin tun daga firamare, sakandare har zuwa manyan makarantu.

Yawancin masana a bangaren ilimi basu yi mamakin ganin jami’o’in Nijeriya basu tabuka abin a zo a gani ba a tantancewa tare da matsayin su a tsakanin jami’o’in duniya, wannan yana faruwa ne saboda yawan yajin aikin da malaman jami’a ke shiga wanda ke haifar da cikas a abin da ya shafi bincike da karantarwa, fiye da wata 4 kenan malaman jami’o’i a Nijeriya ke yajin aiki har yanzu ba a kai ga warware matsalar ba.

A karkashin wannan gwamnatin kawai Malaman Jami’a sun yi yajin aiki na fiye da wata 13, wannan ba karamin asara ba ne ga harkar ilimi a Nijeriya.

Wadannan na daga cikin matsalolin da suka haifar da tabarbarewar ilimi a kasar nan kuma in har ba a magance su ba lamarin ilimi zai cigaba da tabarbarewa a kullum, hakan kuma abin kunya ne ga Nijeriya a idon duniya.

Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun 'Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.