ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsayin Jami’o’in Nijeriya A Ma’aunin Jami’o’in Duniya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
4 years ago
Nijeriya

Fiye da wani lokaci, rahoton da aka fitar na matsayin jami’o’in Nijeriya a ma’aunin jami’o’i na duniya ya nuna cewa, wannan ne lokaci fiye da wani lokacin da ake bukatar a maida da hankali a kan halin da harkar ilimi ta ciki a kasar nan musamman ilimin jami’a a kasar nan.

Rahoton da Cibiyar ‘Times Higher Education’ ta fitar ya nuna cewa, gwarzuwar jami’a a Nijeriya ita ce, Jami’ar Afe Babalola (ABUAD) da ke Ado-Ekiti, wadda ta yi ta 400 a jerin jami’o’in duniya.

  • 2023: Kwankwaso Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Yi Watsi Da APC Da PDP

Cibiyar ta karbu a fadin duniya saboda sahihancin rahotannin da take fitarwa, cikin abubuwan da take lura dasu wajen yanke hukuncin zabar kwazon jami’a sun hada da abin da ya shafi bangaren karantarwa da bincike da kuma yadda jami’ar ta karbuwa a sassan duniya.

ADVERTISEMENT

Yakamata a fahinci cewa, a shekarar 2022 cibiyar ta nazarci jami’o’i 1, 600 a kasashe 99. Cibiyar ta yi nazarin mukala fiye da Miliyan 108 da kuma kundin bincike da jami’o’i fiye da Miliyan 14.4 ta kuma karbi amsar tambayoyi daga masana fiye da 22,000 a fadin duniya.

Babu wata kasar Afrika data zo cikin jami’o’i na 100 na farko a jerin gwarazan jami’o’i duniya. Gwarzuwar jami’a data fi tsari a Afrika ita ce jami’ar kasar Afirka ta Kudu ‘Unibersity of Cape Town’ inda ta zo ta 183 a duniya. A Nijeriya kuma Jami’ar Ibadan da ta Legas suka zo na 401 da 501.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

A yayin da muke taya Jami’ar ABUAD murnar wannan nasarar, mun lura da cewa, wannan yana nuna irin tsananin yadda harkar ilimi ta tabarbarewar a kasar nan.

Duk da matukar muhimmancinta a wajen tafiyar da tattalin arzikin kasa gwamnatocin da suka gabata sun yi watsi da harkar ilimi, ta hanyar nakasa kasafin kudin da ake tanadar wa bangaren ilimin.

Akwai bukatar a sake nazarin kasafin kudin da jihohin kasar nan 36 ke samar wa bangaren ilimi musamman ma ganin kowacce jiha a halin yanzu ta mallaki jami’a ta kanta. Yayin da hukumar Majalisar Dinkin Duniya ta nemi a ware kashi 25 na kasafin kudin da aka kiyasta kashe ga bangaren ilimi har yanzu Nijeriya bata kai ga samar da kashi 15 ba.

A kasafin kudin shakarar 2022 gwmanatin Nijeriya ta ware wa bangaren ilimi Naira Tiriliyan 1.29 wanda ke nuna cewa kashi 7.9 kenan na kasasfin kudin da aka yi a shekarar. Wannan na nuna cewa an yi wa bangaren ilimi kashi 10 kenan duk kuwa da cewa, Majalisar Dinkin Duniya ta nemi ne aware kashi 25 na kasafin kudin a duk shekara don tallafa wa harkar ilimin al’umma.

Idan za a iya tunawa gwamnatin Buhari ta kasafta kashe Naira Tiriliyan 55.3 don gudanar da harkokin gwamnati a cikin shakara 6 na mulkinta amma Naira Tiriliyan 3.5 kawai aka ware wa bangaren ilimi wanda ke nuna kashin yana kasa da kashi 10, wanda ke nuna karara lamarin ilimi ba abin da gwamnatin ta dauka da muhimmanci bane.

Abin takaici a nan shi ne bangaren ilimi ya yi fama da matsalar kudade ga rashin kayan aiki da kuma karancin albashi ga kuma karancin ma’aikata wanda duk suna taimakawa wajen haifar da matsaloli ga bangaren ilimin tun daga firamare, sakandare har zuwa manyan makarantu.

Yawancin masana a bangaren ilimi basu yi mamakin ganin jami’o’in Nijeriya basu tabuka abin a zo a gani ba a tantancewa tare da matsayin su a tsakanin jami’o’in duniya, wannan yana faruwa ne saboda yawan yajin aikin da malaman jami’a ke shiga wanda ke haifar da cikas a abin da ya shafi bincike da karantarwa, fiye da wata 4 kenan malaman jami’o’i a Nijeriya ke yajin aiki har yanzu ba a kai ga warware matsalar ba.

A karkashin wannan gwamnatin kawai Malaman Jami’a sun yi yajin aiki na fiye da wata 13, wannan ba karamin asara ba ne ga harkar ilimi a Nijeriya.

Wadannan na daga cikin matsalolin da suka haifar da tabarbarewar ilimi a kasar nan kuma in har ba a magance su ba lamarin ilimi zai cigaba da tabarbarewa a kullum, hakan kuma abin kunya ne ga Nijeriya a idon duniya.

Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun 'Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.