Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce ya shiga siyasa ne domin yi wa al’umma hidima, ba don ya saci kudaden jama’a ba.Â
A lokacin da yake magana a wani shirin rediyo, ya jaddada cewa ya yana da rufin asiri tun kafin ya zama gwamna, kuma ya shirya yin rantsuwa da Alkur’ani don tabbatar da gaskiyarsa.
- Akpabio, Kekere-Ekun, Abbas Da Wasu Sun Samu Lambar Girmamawa ta Kasa
- Murnar Ƴanci: Gwamna Fintiri Ya Yafe Wa Fursunoni Biyu
Ya zargi Majalisar Dokokin Jihar Kaduna da yi masa sharri kan zargin shi da mukarrabansa sun wawushe Naira biliyan 423 a lokacin da yake gwamna.
El-Rufai ya nuna takaicinsa kan zargin da ake yi masa da kuma farautar abokan aikinsa ta hannun hukumomin yaki da cin hanci.
Ya bayyana cewa ya bar al’amarin a hannun Allah, kuma bai damu da ya kare kansa a bainar jama’a ba.
Duk da kalubalen shari’a da yake fuskanta, yana ci gaba da harkokinsa na yau da kullum tare da ci gaba da yi wa al’umma hidima.
A nan gaba, El-Rufai ya bayyana cewa bayan ya kammala karatunsa, yana shirin dawowa harkar siyasa a shekarar 2027.
Ya sake tabbatar da kudurinsa na cigaba da yi wa jama’a aiki da kokarin bunkasa ci gaban jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp