• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gobe Alhamis 4 ga watan nan na Mayu, rana ce ta matasan kasar Sin. Saboda haka, a cikin sharhin na yau, bari mu tattauna batun da ya shafi matasa.

Hausawa su kan ce “Karen bana shi ke maganin zomon bana.” Amma dai idan an yaudari matasa, za su iya fadawa kuskure. Misali, wasu matasan kasashen Afirka sun fara daukar ra’ayi maras kyau game da kasar Sin, sakamakon yadda suka yarda da labaran jabu, da wasu kafofin yada labaru na kasashen yamma suka watsa, ba tare da tantance gaskiyarsu ba. Sai dai kuma idan wadannan matasa sun samu damar hulda da kasar Sin da kansu, to, tabbas za su canza ra’ayinsu.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Kungiyar WTO Da Ta Kara Sanya Ido Kan Karan Tsaye Ga Ka’idojin Da Amurka Ta Yi

Cikin shekaru 20 da suka wuce, na gamu da matasan kasashen Afirka da yawa, wadanda suka kulla wata alaka da kasar Sin. Wasunsu na karatu a kasar Sin, wasu suna aiki a kamfanonin kasar Sin dake kasashen Afirka, yayin da kuma wasunsu ke gudanar da ciniki tsakanin bangarorin Sin da Afirka, kuma dukkansu sun samu ci gaba sosai a harkokinsu.

A kwanakin baya na gamu da wata daliba ‘yar Najeriya a garin Jinhua dake gabashin kasar Sin, wadda ta taba koyon Sinanci a wata kwalejin Confusious dake Najeriya, sa’an nan ta samu kudin tallafin karatu don ta yi karatu a kasar Sin. Yanzu tana neman ci gaba da karatun digiri na 2 a kasar. Haka kuma, na tuna da wani saurayin da ya zo daga jihar Kano ta Najeriya, wanda na gamu da shi a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin wasu shekaru da suka wuce.

A lokacin yana zama a birnin Guangzhou, inda yake sayen kayayyaki masu alaka da wayar salula, yana tura su zuwa Najeriya a kai a kai. Ko da yake shekarunsa 20 da wani abu kacal a lokacin, amma ya riga ya mallaki wasu shagunan sayar da wayar salula guda 3 a wasu kasuwannin dake Kano.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Wadannan matasa da suka taba hulda da kasar Sin suna da wasu abubuwa na bai daya. Na farko, dukkansu suna kaunar kasar Sin. Sa’an nan na biyu, sun darajanta zumuntar dake tsakanin Afirka da Sin.

Saboda sun gane wa idanunsu ainihin yadda kasar Sin take, kana sun fahimci cewa, zumunta mai zurfi da hadin gwiwar da ake samu tsakanin Afirka da Sin, na ba su damar raya harkoki na kansu cikin nasara.

Mutanen da suka fahimci halayyar Sinawa sun san cewa, Sinawa na dora muhimmanci kan daukar hakikanin mataki. Saboda haka, idan kasar Sin ta dau niyyar kulla huldar abota tare da kai, to, ba za ta bar huldar ta tsaya kan maganar fatar baki ba kadai.

Wata babbar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka ita ce, kokarin taimakawa kasashen Afirka wajen horar da matasa, ta yadda kasashen za su samu damar raya kansu.

Cikin wasu matakai guda 8 da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawarin aiwatarwa, yayin da kasarsa ke hulda da kasashen Afirka, akwai horar da matasan kasashen Afirka don su samu fasahohin raya aikin gona na zamani, da dabarun da ake bukata domin wadatar da manoma, da koyar da ilimin sana’o’i daban daban ga matasan kasashen Afirka, da kafa cibiyoyin kirkire-kirkire, inda matasan Sin da Afirka za su iya hadin gwiwa da juna a kokarin kirkiro fasahohi, da bude sabbin kamfanoni, da dai sauransu. Duk wadannan matakai na tare da zummar taimakawa matasan kasashen Afirka samun kwarewar aiki, da wayewar kai, ta yadda za su iya raya kansu yadda suke bukata.

Ban da haka kuma, idan an duba yanayin da ake ciki a fannin tattalin arziki, za a san cewa kasar Sin na ba da muhimmiyar gudunmowa ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Kana tsare-tsaren tattalin arzikin Sin da na kasashen Afirka suna iya biyan bukatun junansu.

Saboda haka ana iya hasashen cewa, yayin da tattalin arzikin Sin ke kara samun ci gaba, da tabbatar da ingancin kansa, da neman zamanintarwa, kasar za ta haifar da karin damammaki na raya kai ga dimbin kasashen Afirka, gami da matasan kasashen. Yin amfani da damammakin da kyau, zai zame wa dumbin matasan kasashen Afirka, muhimmin dalilin da ya sa suke iya cika burikan da suka sanya a gaba.

Sai dai abun tambaya shi ne, wadanne ayyuka ne suka kamata matasan kasashen Afirka su yi kokarin gudanarwa a yanzu, ta yadda za su iya yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar?

A ganina za a iya fara da koyon Sinanci, da neman halartar ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka ta fuskar aikin ilimi, da halartar tarukan daukar ma’aikata na kamfanonin kasar Sin dake kasashensu, da dai makamantansu. Duk lokacin da ka fara kulla wata alaka da kasar Sin, to, ra’ayinka game da kasar, da shirinka kan rayuwa da aiki za su canza, cikin wani yanayi mai yakini. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano

Next Post

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

8 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

9 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

10 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

11 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

12 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

13 hours ago
Next Post
Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma'aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.