ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

by Sadiq
3 years ago
Gobara

An ware ranar 4 ga watan Mayun kowace shekara a matsayin ranar tunawa da jam’ian kashe gobara na duniya, tun biyo bayan iftila’in mutuwar wasu jami’an kashe gobara a wani dajin kasar Austrilia.

An ware wannan rana ne don tunawa da kuma karrama jami’an kashe gobara a fadin duniya kan yadda suke jajircewa tare da sadaukar da rayukansu wajen ceto al’umma da kuma dukiyoyinsu.

  • Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano
  • Hukumar NDE Ta Fara Rajistar Marasa Aiki A Sakkwato

Kwanturolan Hukumar Kashe Gobara na Tarayya da ke kula da shiyyar Kano da Jigawa, ACG Ahmad Garba Karaye, wanda ya jagorancin bikin wannan shekarar a Jihar Kano, ya ce wasu daga cikin kyaututtukan da aka ba su, za su kai su asibiti don taimaka wa wanda ke da bukata.

ADVERTISEMENT
Gobara
ACG Karaye da jami’an hukumar a Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano

“Ana girmama gwaraza ne a irin wannan rana ne saboda kokarinsu wajen ganin sun kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

“Ana yin wannan biki ne duk duniya, shi ya sa ake yin sa a ko ina.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“…karfe 12 na rana a duk duniya ana tada jiniya na tsawon minti biyar, wanda ita ake tayar wa idan akwai wani abun gaggawa ko iftila’i da ke bukatar dauki, to haka ake tayar da ita babu abin da ya faru, sai don tunawa mutane da kuma girmama wadannan ma’aikata,” in ji Kwanturolan hukumar a Kano.

Gobara
ACG Karaye lokacin da yake gabatar da kyaututtukan ga ma’aikatan lafiya na asibitin

Kamar kowace shekara take wannan shekarar shi ne; ‘Martaba Jaruman Da Ke Kare Mu’ wanda ke nuna muhimmancin jami’an hukumar kashe gobara.

A irin wannan rana daidaikun mutane na kai kyaututtuka zuwa ga ofishoshin hukumar kashe gobara da ke kusa da su don karrama su kan yadda suke ceton rayukan mutane.

Gobara
Yadda jami’an Hukumar Kashe Gobara na Tarayya ke duba marasa lafiya a asibitin Murtala da ke Kano

Shi ma a nasa jawabin, jami’in hulda da jama’a na hukumar, ASF Nura Abdulkadir Maigida, ya ja hankalin jama’a kan muhimmancin bin matakan kariya daga gobara a muhallansu.

Sannan ya bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa hukumar hadin kai don samun damar yadda za ta wanzar da aikinta cikin sauki.

Daga cikin kayan akwai auduga, bandeji, magunguna da sauran kayan aiki da suka shafi gobara.

A wasu lokutan mutane na kai kyautar kudin don nuna jin dadinsu kan nyadda jami’an hukumar ke taka rawar gani a rayuwar yau da kullum ta al’umma.

Hukumar ta kai ziyara Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano, inda suka duba marasa lafiya da kuma gabatar da kyautar wasu daga cikin kyaututtukan da aka ba su ga asibitin.

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

Jarin Waje Na Sin Na Bunkasa Ci Gaban Kasar Habasha

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.