ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Gobe Alhamis 4 ga watan nan na Mayu, rana ce ta matasan kasar Sin. Saboda haka, a cikin sharhin na yau, bari mu tattauna batun da ya shafi matasa.

Hausawa su kan ce “Karen bana shi ke maganin zomon bana.” Amma dai idan an yaudari matasa, za su iya fadawa kuskure. Misali, wasu matasan kasashen Afirka sun fara daukar ra’ayi maras kyau game da kasar Sin, sakamakon yadda suka yarda da labaran jabu, da wasu kafofin yada labaru na kasashen yamma suka watsa, ba tare da tantance gaskiyarsu ba. Sai dai kuma idan wadannan matasa sun samu damar hulda da kasar Sin da kansu, to, tabbas za su canza ra’ayinsu.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Kungiyar WTO Da Ta Kara Sanya Ido Kan Karan Tsaye Ga Ka’idojin Da Amurka Ta Yi

Cikin shekaru 20 da suka wuce, na gamu da matasan kasashen Afirka da yawa, wadanda suka kulla wata alaka da kasar Sin. Wasunsu na karatu a kasar Sin, wasu suna aiki a kamfanonin kasar Sin dake kasashen Afirka, yayin da kuma wasunsu ke gudanar da ciniki tsakanin bangarorin Sin da Afirka, kuma dukkansu sun samu ci gaba sosai a harkokinsu.

ADVERTISEMENT

A kwanakin baya na gamu da wata daliba ‘yar Najeriya a garin Jinhua dake gabashin kasar Sin, wadda ta taba koyon Sinanci a wata kwalejin Confusious dake Najeriya, sa’an nan ta samu kudin tallafin karatu don ta yi karatu a kasar Sin. Yanzu tana neman ci gaba da karatun digiri na 2 a kasar. Haka kuma, na tuna da wani saurayin da ya zo daga jihar Kano ta Najeriya, wanda na gamu da shi a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin wasu shekaru da suka wuce.

A lokacin yana zama a birnin Guangzhou, inda yake sayen kayayyaki masu alaka da wayar salula, yana tura su zuwa Najeriya a kai a kai. Ko da yake shekarunsa 20 da wani abu kacal a lokacin, amma ya riga ya mallaki wasu shagunan sayar da wayar salula guda 3 a wasu kasuwannin dake Kano.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Wadannan matasa da suka taba hulda da kasar Sin suna da wasu abubuwa na bai daya. Na farko, dukkansu suna kaunar kasar Sin. Sa’an nan na biyu, sun darajanta zumuntar dake tsakanin Afirka da Sin.

Saboda sun gane wa idanunsu ainihin yadda kasar Sin take, kana sun fahimci cewa, zumunta mai zurfi da hadin gwiwar da ake samu tsakanin Afirka da Sin, na ba su damar raya harkoki na kansu cikin nasara.

Mutanen da suka fahimci halayyar Sinawa sun san cewa, Sinawa na dora muhimmanci kan daukar hakikanin mataki. Saboda haka, idan kasar Sin ta dau niyyar kulla huldar abota tare da kai, to, ba za ta bar huldar ta tsaya kan maganar fatar baki ba kadai.

Wata babbar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka ita ce, kokarin taimakawa kasashen Afirka wajen horar da matasa, ta yadda kasashen za su samu damar raya kansu.

Cikin wasu matakai guda 8 da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawarin aiwatarwa, yayin da kasarsa ke hulda da kasashen Afirka, akwai horar da matasan kasashen Afirka don su samu fasahohin raya aikin gona na zamani, da dabarun da ake bukata domin wadatar da manoma, da koyar da ilimin sana’o’i daban daban ga matasan kasashen Afirka, da kafa cibiyoyin kirkire-kirkire, inda matasan Sin da Afirka za su iya hadin gwiwa da juna a kokarin kirkiro fasahohi, da bude sabbin kamfanoni, da dai sauransu. Duk wadannan matakai na tare da zummar taimakawa matasan kasashen Afirka samun kwarewar aiki, da wayewar kai, ta yadda za su iya raya kansu yadda suke bukata.

Ban da haka kuma, idan an duba yanayin da ake ciki a fannin tattalin arziki, za a san cewa kasar Sin na ba da muhimmiyar gudunmowa ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Kana tsare-tsaren tattalin arzikin Sin da na kasashen Afirka suna iya biyan bukatun junansu.

Saboda haka ana iya hasashen cewa, yayin da tattalin arzikin Sin ke kara samun ci gaba, da tabbatar da ingancin kansa, da neman zamanintarwa, kasar za ta haifar da karin damammaki na raya kai ga dimbin kasashen Afirka, gami da matasan kasashen. Yin amfani da damammakin da kyau, zai zame wa dumbin matasan kasashen Afirka, muhimmin dalilin da ya sa suke iya cika burikan da suka sanya a gaba.

Sai dai abun tambaya shi ne, wadanne ayyuka ne suka kamata matasan kasashen Afirka su yi kokarin gudanarwa a yanzu, ta yadda za su iya yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar?

A ganina za a iya fara da koyon Sinanci, da neman halartar ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka ta fuskar aikin ilimi, da halartar tarukan daukar ma’aikata na kamfanonin kasar Sin dake kasashensu, da dai makamantansu. Duk lokacin da ka fara kulla wata alaka da kasar Sin, to, ra’ayinka game da kasar, da shirinka kan rayuwa da aiki za su canza, cikin wani yanayi mai yakini. (Bello Wang)

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
Next Post
Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma'aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.