• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
A Yi Kokarin Yin Amfani Da Damammakin Da Kasar Sin Ta Samar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gobe Alhamis 4 ga watan nan na Mayu, rana ce ta matasan kasar Sin. Saboda haka, a cikin sharhin na yau, bari mu tattauna batun da ya shafi matasa.

Hausawa su kan ce “Karen bana shi ke maganin zomon bana.” Amma dai idan an yaudari matasa, za su iya fadawa kuskure. Misali, wasu matasan kasashen Afirka sun fara daukar ra’ayi maras kyau game da kasar Sin, sakamakon yadda suka yarda da labaran jabu, da wasu kafofin yada labaru na kasashen yamma suka watsa, ba tare da tantance gaskiyarsu ba. Sai dai kuma idan wadannan matasa sun samu damar hulda da kasar Sin da kansu, to, tabbas za su canza ra’ayinsu.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Kungiyar WTO Da Ta Kara Sanya Ido Kan Karan Tsaye Ga Ka’idojin Da Amurka Ta Yi

Cikin shekaru 20 da suka wuce, na gamu da matasan kasashen Afirka da yawa, wadanda suka kulla wata alaka da kasar Sin. Wasunsu na karatu a kasar Sin, wasu suna aiki a kamfanonin kasar Sin dake kasashen Afirka, yayin da kuma wasunsu ke gudanar da ciniki tsakanin bangarorin Sin da Afirka, kuma dukkansu sun samu ci gaba sosai a harkokinsu.

A kwanakin baya na gamu da wata daliba ‘yar Najeriya a garin Jinhua dake gabashin kasar Sin, wadda ta taba koyon Sinanci a wata kwalejin Confusious dake Najeriya, sa’an nan ta samu kudin tallafin karatu don ta yi karatu a kasar Sin. Yanzu tana neman ci gaba da karatun digiri na 2 a kasar. Haka kuma, na tuna da wani saurayin da ya zo daga jihar Kano ta Najeriya, wanda na gamu da shi a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin wasu shekaru da suka wuce.

A lokacin yana zama a birnin Guangzhou, inda yake sayen kayayyaki masu alaka da wayar salula, yana tura su zuwa Najeriya a kai a kai. Ko da yake shekarunsa 20 da wani abu kacal a lokacin, amma ya riga ya mallaki wasu shagunan sayar da wayar salula guda 3 a wasu kasuwannin dake Kano.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Wadannan matasa da suka taba hulda da kasar Sin suna da wasu abubuwa na bai daya. Na farko, dukkansu suna kaunar kasar Sin. Sa’an nan na biyu, sun darajanta zumuntar dake tsakanin Afirka da Sin.

Saboda sun gane wa idanunsu ainihin yadda kasar Sin take, kana sun fahimci cewa, zumunta mai zurfi da hadin gwiwar da ake samu tsakanin Afirka da Sin, na ba su damar raya harkoki na kansu cikin nasara.

Mutanen da suka fahimci halayyar Sinawa sun san cewa, Sinawa na dora muhimmanci kan daukar hakikanin mataki. Saboda haka, idan kasar Sin ta dau niyyar kulla huldar abota tare da kai, to, ba za ta bar huldar ta tsaya kan maganar fatar baki ba kadai.

Wata babbar manufar kasar Sin ta fuskar hulda da kasashen Afirka ita ce, kokarin taimakawa kasashen Afirka wajen horar da matasa, ta yadda kasashen za su samu damar raya kansu.

Cikin wasu matakai guda 8 da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi alkawarin aiwatarwa, yayin da kasarsa ke hulda da kasashen Afirka, akwai horar da matasan kasashen Afirka don su samu fasahohin raya aikin gona na zamani, da dabarun da ake bukata domin wadatar da manoma, da koyar da ilimin sana’o’i daban daban ga matasan kasashen Afirka, da kafa cibiyoyin kirkire-kirkire, inda matasan Sin da Afirka za su iya hadin gwiwa da juna a kokarin kirkiro fasahohi, da bude sabbin kamfanoni, da dai sauransu. Duk wadannan matakai na tare da zummar taimakawa matasan kasashen Afirka samun kwarewar aiki, da wayewar kai, ta yadda za su iya raya kansu yadda suke bukata.

Ban da haka kuma, idan an duba yanayin da ake ciki a fannin tattalin arziki, za a san cewa kasar Sin na ba da muhimmiyar gudunmowa ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Kana tsare-tsaren tattalin arzikin Sin da na kasashen Afirka suna iya biyan bukatun junansu.

Saboda haka ana iya hasashen cewa, yayin da tattalin arzikin Sin ke kara samun ci gaba, da tabbatar da ingancin kansa, da neman zamanintarwa, kasar za ta haifar da karin damammaki na raya kai ga dimbin kasashen Afirka, gami da matasan kasashen. Yin amfani da damammakin da kyau, zai zame wa dumbin matasan kasashen Afirka, muhimmin dalilin da ya sa suke iya cika burikan da suka sanya a gaba.

Sai dai abun tambaya shi ne, wadanne ayyuka ne suka kamata matasan kasashen Afirka su yi kokarin gudanarwa a yanzu, ta yadda za su iya yin amfani da damammakin da kasar Sin ta samar?

A ganina za a iya fara da koyon Sinanci, da neman halartar ayyukan hadin gwiwar Sin da Afirka ta fuskar aikin ilimi, da halartar tarukan daukar ma’aikata na kamfanonin kasar Sin dake kasashensu, da dai makamantansu. Duk lokacin da ka fara kulla wata alaka da kasar Sin, to, ra’ayinka game da kasar, da shirinka kan rayuwa da aiki za su canza, cikin wani yanayi mai yakini. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano

Next Post

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Related

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli
Daga Birnin Sin

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

5 hours ago
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

7 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

8 hours ago
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka
Daga Birnin Sin

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

8 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

9 hours ago
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

11 hours ago
Next Post
Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma’aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

Yadda Aka Yi Bikin Tunawa Da Ma'aikatan Kashe Gobara Na Duniya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.