• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abba Ya Gabatar Da Kwarya-kwaryar Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 99 Ga Majalisar Kano

by Naziru Adam Ibrahim
10 months ago
in Labarai
0
Abba Ya Gabatar Da Kwarya-kwaryar Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 99 Ga Majalisar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya rubuta wa majalisar dokokin jihar takardar neman amincewarta da kasafin kudin shekarar 2024 na karin kudi, N99, 221,503,569.90.

Bukatar gwamnan na kunshe ne cikin wata wasiƙa da aka karanta a zauren majalisar a yayin zaman da shugaban majalisar, Ismail Falgore ya jagoranta.

  • Ambaliya Ta Yi Ajalin Mutane 49 A Arewa Maso Gabas – NEMA
  • Gwamnan Nasir Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Naira Biliyan 6.5 Ga Mutane 65,000 A Kebbi

Yayin da yake karanta wasikar, Falgore ya bayyana cewa gwamnan yana neman amincewarsu ne bisa bin sashe na 122 (A da B) na kundin tsarin mulkin ƙasar nan na 1999, don ƙara kaimi da aiwatar da ayyukan da suka sa gaba na inganta rayuwar al’ummar jihar.

Ya kuma bayyana cewa, daga cikin kasafin kudin, an ware kimanin Naira biliyan 34 na kudin ma’aikata da wata 35 na shirin ko ta kwana da kuma na sama da biliyan 31 don gudanar da ayyuuka.

Da yake zantawa da manema labarai bayan gabatar da wasikar ga majalisar, kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi na jihar, Musa Shanono, ya ce, kasafin farko na jihar na 2024 ya kai Naira biliyan 438 idan an hada da wannan karin kasafin da ake neman amincewa da shi a doka, zai kawo kasafin 2024 zuwa naira biliyan 537.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Yayin da yake nanata kudirin gwamnatin na mayar da hankali kan raya ababen more rayuwa da bunkasa walwala da ma inganta fannin lafiya da ilimi, Shanono ya jaddada cewa ƙarin kasafin kudin zai kunshi sabon mafi karancin albashi da dai sauransu.

Shi ma ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Nassarawa Yusuf Aliyu, ya nemi goyon bayan sauran ‘yan majalisar don yin kira ga Gwamna Yusuf da ya gyara tare da sake gina filin wasa na Gwagwarwa da ke unguwar Gawuna a ƙaramar hukumar Nassarawa, don yakar ta’addancin da ake samu da safarar miyagun kwayoyi a filin wasan, da rashin tsaro a tsakanin al’umma.

A cewar Aliyu, mummunan halin da filin wasan ke ciki ya sanya wajen ya koma mafakar bata gari kuma abin tsoro ga mazauna yankin wanda gyara shi zai inganta tsaron al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbakanoKasafin Kuɗi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliya Ta Yi Ajalin Mutane 49 A Arewa Maso Gabas – NEMA

Next Post

Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Related

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

2 hours ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

3 hours ago
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

10 hours ago
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2
Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

10 hours ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

12 hours ago
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Manyan Labarai

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

15 hours ago
Next Post
Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

June 24, 2025
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

June 24, 2025
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

June 24, 2025
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.