• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abdullahi Adamu Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Abdullahi Adamu Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya mika takardar ajiye mukaminsa a daren ranar Lahadi, kamar yadda rahotanni suka tabbatar da hakan.

Wata majiya ta tabbatar wa da cewa Adamu, wanda ya zama shugaban jam’iyyar na kasa a babban taron jam’iyyar na kasa da aka gudanar cikin watan Maris din shekarar 2022, ya aike da takardar murabus dinsa zuwa fadar shugaban kasa ta da ke Abuja gabanin dawowar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu daga taron kungiyar tarayyar Afrika (AU) a kasar Kenya.

  • Rikicin APC: Kujerar Abdullahi Adamu Tana-kasa-tana-dabo
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Daya daga cikin majiyar ta ce Adamu, tsohon gwamnan jihar Nasarawa, ya aika wasikar murabus din ga shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, da misalin karfe 4 na yammacin ranar Lahadi.

Kazalika, wata majiya daga bangaren Adamu ta tabbatar da hakan, inda ta kara da cewa, “Shugaban Jam’iyyar APC na kasa ya yi murabus ne biyo bayan samun wasu bayanai na wasu mutane makusanta shugaban kasa da suke shirin tozarta shi a taron jam’iyyar da za a yi ranar Laraba.”

Sai dai majiyar ta musanta wani rahoto da ke cewa shugaba Tinubu ne ya bukaci Adamu ya yi murabus gabanin taron majalisar zartarwa na jam’iyyar na kasa da za a yi ranar Laraba. Jam’iyyar ta tsayar da ranakun 10 da 11 ga watan Yuli domin gudanar da tarukan kwamitinta na kasa da na NEC domin warware matsalolin da suka shafi rikicin kwamitin gudanarwar Jam’iyyar na kasa (NWC).

Labarai Masu Nasaba

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

Sai dai daga baya an dage tarukan da aka shirya zuwa ranar Larabar nan.

Wani mamba a jam’iyyar ya ce, Adamun ya yi murabus ne a lokacin da ya bayanan shirin wasu mutane biyu masu fada a ji a kusa da shugaban kasar na shirin kulla masa tuggun siyasa da tozarta shi.

“Ya yi murabus ne saboda sun fara sanya hannu don tsige shi a tarurrukan Jam’iyyar da za a gabatar. Ya yi murabus ne domin ya tseratar da kansa daga wulakanci,” cewar dan Jam’iyyar

Da aka tuntubi Adamu, ya shaida cewa ba zai ce uffan ba kan lamarin har sai Shugaba Tinubu ya dawo daga taron AU.

“Ba zan yi magana kan wannan batun ba saboda shugaban kasa ba ya nan,” in ji Adamu

Idan dai ba a manta ba, tun da jimawa gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC, Adamu ya ayyana tsohon shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a matsayin dan takarar jam’iyyar a shugabancin kasa.

Wannan furuci da Adamu ya yi ya haifar da hargitsi a cikin jam’iyyar a wancan lokacin, yayin da gwamnonin jam’iyyar daga Arewa suka rufar masa suna masu nuna goyan bayansu game Tinubu.

Matsayin gwamnonin ya tilastawa jam’iyyar bude koffar neman tikitin takarar shugaban kasa ga kowa, inda Tinubu ya lashe zaben.

Ko a kwanakin nan an jiyo, Adamu na sukar jerin sunayen shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da kakakin majalisar, Tajudeen Abbas, kan sunayen da suka bayyana a matsayin shugabancin majalisun biyu.

Bayan faruwar lamarin, shugaba Tinubu ya gayyaci Adamu zuwa fadar fadar shugaban kasa, inda aka warware matsalolin a yayin zaman.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi AdamuAPCShugabancin Jam'iyyar APCTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Pulaku: Tinubu Zai Magance Rikicin Arewa Maso Yammacin Nijeriya —Shettima

Next Post

Shehun Borno Ya Bukaci Jama’ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

Related

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

17 hours ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

22 hours ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

1 day ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

1 day ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

1 day ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

2 days ago
Next Post
Shehun Borno Ya Bukaci Jama’ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

Shehun Borno Ya Bukaci Jama'ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.