• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin APC: Kujerar Abdullahi Adamu Tana-kasa-tana-dabo

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rikicin APC: Kujerar Abdullahi Adamu Tana-kasa-tana-dabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gabanin taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar APC na kasa da aka shirya gudanarwa a ranakun 18 da 19 ga watan Yuli, wani yanayi na nuna rashin tabbas game da makomar kujerar shugaban jam’iyyar na kasa Abdullahi Adamu.

Kamar yadda ya taba faruwa da tsohon shugaban jam’iyyar Adams Oshiomhole.

  • Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
  • Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega

Adamu wanda ya zama shugaban APC na kasa a yayin gangamin wani taron jam’iyyar na kasa da kwamitin rikon kwarya da gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya shirya a dandalin ‘Eagles Skuare’ da ke Abuja a watan Maris ta 2022, yana fama da matsin lamba kan ya ajiye mukaminsa bisa zarginsa da ake yi na wawuce kudaden jam’iyya ba bisa ka’ida ba.

Tsohon gwamnan na Jihar Nasarawa, Adamu ya samu goyon bayan tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari kuma a dalilin haka ne aka bukaci sauran masu neman takarar shugabancin jam’iyyar su janye masa.

Sai dai tun a farkon wa’adinsa na shekaru hudu a kan kujerar shugabancin jam’iyyar ya hadu tarnaki, a daidai lokacin da wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar suka yi kira da ya yi murabus domin daidaita madafun iko ta bangaren addini.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

A yayin da ake fargabar cewa kwamitin zartarwar jam’iyyar ta kasa, wadda shi ne na biyu mafi girma a jam’iyyar, zai iya goya masa baya sakamakon wasu zarge-zarge da suka shafi kudade da wasu abubuwa, kan haka Adamu ya gana da shugabannin jam’iyyar na jihohi a Abuja.

Ganawar ta gudana ce a shalkwatan jam’iyyar APC ta kasa a wani kokarin da shugaban jam’iyyar yake yi na neman goyon baya daga wurin shugabannin jam’iyyar na jihohi gabannin taron kwamitin zartarwar na kasa.

Idan za a iya tuna shugabannin jam’iyyar APC na jihohi dukkansu mambobin kwamitin zartarwa ne kuma suna iya kada kuri’ar rashin amincewa da shugaban.

Wani dan jam’iyyar APC na kasa wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “Babu wanda ya san abin da zai faru. Akwai mutanen da ba sa son salon shugabancin Adamu, akwai kuma masu rura wutar rikici da rashin jutuwa a cikin jam’iyyar.

“A wancan lokacin, Adamu bai goyi bayan Tinubu ba, amma muka yi galaba a kansa, saboda mun ci zabe kuma lokaci ya yi da za mu hada kan jam’iyyar, sannan kuma wannan lokaci ne da za mu hada kan kasar nan.

“Tinubu ba ya tunanin korar Adamu a yanzu saboda ya yi wuri da yawa. Adamu zai iya yin murabus da kansa idan har ya ci gaba da samun matsin lamba.

“Idan Tinubu ya ga dama zai iya kula da sha’anin jam’iyyar, Adamu ba zai iya yin komai ba. Idan Tinubu ya yanke shawarar amsar ragamar shugabancin jam’iyyar, Adamu zai iya karbar umarni ne kawai daga gare shi. Don haka ba za a sami rikicin tsige Adamu ba.”

Wata majiyar ta ce da a ce za a tsige Adamu, da Tinubu bai nada tsohon gwamnan Jihar Benuwai, Sanata George Akume a matsayin sakataren gwamnatin tarayya ba.

Majiyar ta kara da cewa nadin Akume manuniyace ba za a tsige Adamu ba a yanzu.

Ta ce, “Siyasa ‘yar lissafi ce. Wani lokaci a yi nasara, sannan wani lokaci a samu rashin nasara.

“Duba da cewa da ba a nada Akume a matsayin sakataren gwamnatin tarayya ba, da an ba shi matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa idan an tsige Adamu a lokacin taron kwamitin gudanarwa na jam’iyyar.

“Idan za a iya tuna, shugaban kasa ne kawai zai iya tsige shi ko ya yi murabus. Idan shugaban kasa ba ya bukatarsa, yana da ikon tara mambobin kwamitin zartarwa su jefa kuri’ar rashin amincewa.”

Idan dai za a iya tunawa, mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa a yankin Arewa maso yamma, Salihu Mohammed Lukman, ya bukaci Adamu ya yi murabus domin wani kirista ya karbi ragamar shugabancin jam’iyyar.

Da yake jawabi ga manema labarai bayan kammala taron da Adamu, shugaban jam’iyyar na Jihar Kuros Riba kuma mukaddashin sakataren kungiyar shugabannin APC, Alphonsus Oga, ya ce kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC ya gayyace su domin gudanar da taron.

Sai dai ya musanta duk wani nau’i na rikici a jam’iyyar a matsayin dalilin dage taron kwamitin gudanarwa na jam’iyyar.

Ya ce, “Kamar yadda kuka sani, tun bayan zaben da muka yi nasara, ba mu samu damar ganawa da shugabanninmu da shugabanmu na kasa da mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ba.

“Mun samu damar gudanar da taron da aka shirya ne bisa gayyatar da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya aika mana, kuma muna farin cikin sanar da ku cewa wannan wata dama ce ga shugabannin jam’iyyar APC na jihohi domin taya murna ga shugaban jam’iyyarmu mai girma, Sanata Abdullahi Adamu da tawagarsa masu himma wajen gudanar da aiki tukuru da suke yi.”

Da aka tambaye shi ko an dage taron na kwamitin zartarwa ne saboda sabon rikicin da ya kunno kai, Oga ya ce, “Wannan lokaci ne na jita-jita da zage-zage za su karu, amma jam’iyya APC a dunkule take, kuma mun sake haduwa ne domin bayar da goyon baya ga shugabanmu na kasa kuma mambobin kwamitin gudanarwa.

Da yake jawabi yayin bude taron, Adamu ya roki Shugaba Tinubu ya karfafa jam’iyyar.

Ya ce, “Muna fata tare da gudanar da addu’o’i cewa mai girma shugaban kasa ya yi aiki kafada da kafada da mu wajen karfafa dangantakar jam’iyyar a jihohi da ma kasa baki daya don samun wata sabuwar gwamnati nan gaba.

“Wadannan su ne muhimman batutuwan da muke fatan cimmawa tare da ku a yayin wannan taron.

“Mun yi tunanin cewa taron da muka yi da ku a matsayinku na shugabannin da ke da alhaki, ba shakka gwamnonin su ne jagororin jam’iyyarmu a jihohi, amma kuna tafiyar da jam’iyyar a kullum da kyakkyawar fahimtar juna a tsakaninku da gwamnoni da mambobin kwamitin gudanarwa na kasa kamar yadda aka saba wajen inganta shugabancin da muke son yi wa jam’iyyar.”

Adamu ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa jam’iyyar za ta lashe zaben gwamnonin jihohin Bayelsa, Kogi da Imo da aka shirya gudanarwa a watan Nuwamba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCRikiciTambarin Dimokuradiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro

Next Post

Kotu Ta Wanke Mendy Daga Laifin Fyade

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Kotu Ta Wanke Mendy Daga Laifin Fyade

Kotu Ta Wanke Mendy Daga Laifin Fyade

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.