• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu dai ba labari ba ne cewa al’amura suna shirin kwabe wa tsarin rabon shugabancin jam’iyyar APC mai mulki, biyo bayan koma-bayan da jam’iyyar ta samu kan batun rarraba mukami na shiyya-shiyen a shugabancin majalisar ta 10 da jam’iyyar ta fitar a ranar Litinin da ta gabata.

Bisa la’akari da yadda lamarin ke kara kamari, zaman lafiya da kwanciyar hankali da ake samu a cikin jam’iyyar na gab da rugujewa a yayin da zababbun ‘yan majalisar da aka zaba su a karkashin inuwar jam’iyyar suka yi barazanar tayar da kayar baya idan ba a sake duba tsarin shiyya-shiyya mai cike da ce-ce-ku-ce ba daga kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ta kasa.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Zambia Ta Shirya Jan Hankalin Sinawa Masu Zuba Jari

Shugabancin jam’iyyar a hukumance ya tabbatar da amincewa da tsohon ministan harkokin Neja Delta, Sanata Godwill Akpabio, (daga Jihar Akwa Ibom a kudu maso kudu) a matsayin shugaban majalisar dattawa, da Tajudeen Abbas (daga Jihar Kaduna a Arewa maso yamma) a matsayin shugaban majalisar wakilai.

‘Yan majalisar da suka fusata sun bayyana salon shiyya-shiyya mai cike da ce-ce-kuce a matsayin wanda ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar kuma bai dace da tsarin dimokuradiyya ba. Suna da ra’ayin cewa bai kamata jam’iyyar ta karkata zuwa yankin maimakon duba kananan shiyya ga daidaikun mutane.

Idan dai za a iya tunawa, wasu masu neman kujerar kakakin majalisar wakilai da zababbun ‘yan majalisa da dama ne suka fara yi wa lamarin bore yayin ganawarsu da Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdulahi Adamu a ranar Larabar da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Daukaka Kara Ta Samu Korafe-korafen Zabubbukan 2023 Guda 1,209

Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

Sun kuma yi barazana ga shugabancin jam’iyyar da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar kan kar su maimaituwa kuskuren 2015 idan jam’iyyar ta bar tsarin shiyyar da ta dage a kan shi ba. Sanatoci da ‘yan majalisar wakilai a shekarar 2015 sun bijire wa zabin jam’iyya mai mulki tare da zabar nasu ‘yan takara masu zaman kansu a manyan mukamai a majalisun tarayya guda biyu.

Wadanda suka tsaya takarar shugaban majalisar wakilai da zababbun ‘yan majalia a taron sun kasance karkashin jagorancin mataimakin kakakin majalisar, Hon. Idris Wase.

Wadanda suka tsaya a wurin taron sun hada da Hon. Yusuf Gagdi, Hon. Muktar Betara, Hon. Ahmed Jaha, Hon. Femi Bamishile, Hon. Abubakar Nakraba, Hon. Mariam Onuaha, Hon. Sani Jaji, Hon. Sada Soli da kuma Hon. Mariam Onuoha.

Hakazalika, a ranar Alhamis da ta gabata tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Abdulaziz Yari, da babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Kalu, da Sanata Osita Izunaso da Sanata Sani Musa suka mika takardar bore a lokacin wata ganawa da Adamu da sauran mambobin kwamitin gudanarwa, inda suka nuna rashin jin dadinsu kan tsarin shiyya-shiyya da jam’iyyar ta fitar.

Sun yi gargadin cewa jam’iyyun adawa na iya samun nasara idan ba a sake duba tsarin shiyya-shiyya da jam’iyyar ta fitar ba.

Yari ya ce Arewa za ta yanke shawara idan ba a sake duba yarjejeniyar shiyyar ba, yayin da Musa ya ce dole ne a gyara rashin adalcin da ke tattare da shirin shiyya-shiyya, inda Kalu ya sha alwashin za su kalubalanci tsarin shiyya-shiya da ake shirin yi.

Dangane da barazanar da kuma bacin ran da ya biyo bayan tsarin shiyyar, Adamu ya roki fusatattun sanatocin da suka kwantar da hankalinsu, yana mai cewa shugabannin APC za su sake duba tsarin shiyya. Ya yarda cewa ba a tuntubi ‘yan majalisar yadda ya kamata ba.

To sai dai kuma duk da cewa jam’iyya mai mulki na iya samun nasara a zauren majalisar dattawa, amma a majalisar wakilai lamarin ba haka yake ba, saboda jam’iyyun adawa ke da rinjayen a zauren majalisar.

Wani abin sha’awan shi ne, jam’iyyun adawa da suka hada da PDP, NNPP, SDP, LP da sauran su ne ke da rinjaye a majalisar da kujeru 180, yayin da APC ke da 178. Kujeru guda biyu ne ake jira, daya daga Akwa Ibom saura kuma daga jihohin Ondo.

Duk da cewa jam’iyyar ta amince da Abbas a matsayin kakakin majalisar wakilai, Muktar Betara, wanda ke wakiltar mazabar Biu/Bayo/Shani ta Jihar Borno, shi ne mutumin da zai iya lashe wannan mukami bisa irin farin jinin da yake samu a tsakanin takwarorinsa ‘yan majalisa.

Dan majalisar na Borno wanda ya bayyana kaduwarsa kan zaben da jam’iyyar ta yi na shugaban majalisar, ya ce babu wanda zai sa shi ya janye takararsa.

A ganawar da yayi da kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC a ranar Larabar da ta gabata, Betara ya ce babu wani lokacin da aka ware ga mukaman shugabanni majalisu guda biyu zuwa yanki daya.

Betara ya jaddada rashin amincewarsa da matakin na kakaba shugaban majalisar wakilai, yana mai cewa za su iya amince da wani dan takarar ne kawai da aka amince da shi bisa yarjejeniya.

Hakazalika, Gagdi ya yi kashedi game da kakaba shugabancin majalisar daga wajen zauren majalisa.

A cewarsa, “Muna da kudurin aniyar kare dimokuradiyya. Majalisar wakilai ita ce majalisar al’ummar Nijeriya. A lokacin da muka fara aiki gadan-gadan, babu shugabancin jam’iyyar da zai kasance a wurin. Mu za mu dukufa wajen gudanar da ayyukan yin doka”

A kwanakin baya ne wasu zababbun ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar PDP, LP, NNPP da APC suka yi taro a Abuja, inda suka yanke shawarar cewa ba za su mutunta matakin da APC ta dauka na shiyya-shiyya ba, amma suna goyon bayan Betara.

Haka kuma sun yi nuni da cewa kasancewar zababben mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya fito ne daga yankin Arewa maso gabas bai hana Betara ya zama shugaban majalisar wakilai ba idan aka yi la’akari da tarihinsa da gogewarsa da kuma ayyukansa a karo na hudu a zauren majalisa.

An fara zaben Betara ne a shekara ta 2007. A matsayinsa na shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisar, ya nuna himma, tsantseni da kwarewa a matsayinsa wanda ya rike mukamin mai gudanarwa da kuma kula da albarkatu na cikin tsarin kasafin kudi yana ba da gudummawa wajen bincikar ayyukan da suka dace a kan al’amurar kasafin kudi.

Betara ya gudanar da ayyuka a mazabarsa ta fuskar aiwatar da makilci nigari. Ya sami damar gudanar da dibin ayyuka don taimaka wa al’ummar mazabarsa wajen dakile musu matsalolin da suka addabe su.

Ayyukan da ya gudanar sun hada da gina kananan filayen wasanni har guda biyar na wucin-gadi a kananan hukumomin Biu, Bayo, Shani da Kwaya- kusar a Jihar Borno da gina cibiyar kula da cutar daji a Maiduguri da gina tituna samu nisan kilomita 80 a kananan hukumomin Biu, Bayo, Kwaya-kusar da Shani da gyarawa da gina sabbin ofisoshin ‘yansanda a kananan hukumomin Biu da Kwaya da gina gidajen zamani na jami’an DSS da sauran jami’an tsaro a kananan hukumomin Biu da Kwaya kusar da dai sauransu.

Zababben dan majalisar mai wakiltar mazabar Obudu/Obanliku/Bekwara na Jihar Kuros Ribas, Peter Akpanke na jam’iyyar PDP, wanda ya yi magana a madadin takwarorinsa na yankin kudu maso kudu bayan taron ya ce tsarin shiyya-shiyya na jam’iyya mai mulki ba zai haifar da da mai ido ba.

Ya ce, “Dukkanmu ba ’yan jam’iyyar APC ba ne, don haka duk abin da suka yanke ba zai zama mai tasiri a kanmu ba. Wannan shi ne shawarar jam’iyyarsu.

Idan za su iya shawo kan membobinsu, hakan yana da kyau a gare su. Amma ba su da yawa, mu ‘yan adawa mun fi yawa. Suna bukatar mu kafin su iya samar da shugaban majalisar wakilai. Mun san cewa ba duk ‘ya’yan jam’iyyar APC ba ne ke goyon bayan matakin da jam’iyyar ta dauka ba.

Yayin da jam’iyya mai mulki za ta bukaci a sake duba tsarin shiyya-shiyya, amma shugabannin jam’iyyar su na jiran zababben shugaban kasa wanda ba ya kasar ya tantance hanyar da za a bi. Duk wani abu da ba a yi nazari ba zai ga gwamnati mai shigowa ta fara kan hanyar da ba ta dace ba, wanda dole ne a kauce masa.

Tags: AkpabioMajalisa Ta 10Tajuddeen
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jadawalin Tsare-Tsaren Bikin Mika Mulki Daga Shugaba Buhari Zuwa Bola Tinubu

Next Post

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

Related

Kotun Daukaka Kara Ta Samu Korafe-korafen Zabubbukan 2023 Guda 1,209
Tambarin Dimokuradiyya

Kotun Daukaka Kara Ta Samu Korafe-korafen Zabubbukan 2023 Guda 1,209

2 days ago
Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

2 days ago
Akpabio
Tambarin Dimokuradiyya

Munakisar Da Ke Cikin Batun Tsige Akpabio

1 week ago
Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

1 week ago
Kotu
Tambarin Dimokuradiyya

Martanin Da Ya Biyo Bayan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnonin Kano, Bauchi Da Zamfara 

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

2 weeks ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

LABARAI MASU NASABA

Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Gwamnatin Tarayya Ta Yaba Da Ayyukan Bello Koko Na Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kafa Sashi Na Musamman A NPA Don Inganta Ayyukanta

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.