ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abdullahi Adamu Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

by Muhammad
3 years ago
Abdullahi

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya mika takardar ajiye mukaminsa a daren ranar Lahadi, kamar yadda rahotanni suka tabbatar da hakan.

Wata majiya ta tabbatar wa da cewa Adamu, wanda ya zama shugaban jam’iyyar na kasa a babban taron jam’iyyar na kasa da aka gudanar cikin watan Maris din shekarar 2022, ya aike da takardar murabus dinsa zuwa fadar shugaban kasa ta da ke Abuja gabanin dawowar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu daga taron kungiyar tarayyar Afrika (AU) a kasar Kenya.

  • Rikicin APC: Kujerar Abdullahi Adamu Tana-kasa-tana-dabo
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Daya daga cikin majiyar ta ce Adamu, tsohon gwamnan jihar Nasarawa, ya aika wasikar murabus din ga shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, da misalin karfe 4 na yammacin ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

Kazalika, wata majiya daga bangaren Adamu ta tabbatar da hakan, inda ta kara da cewa, “Shugaban Jam’iyyar APC na kasa ya yi murabus ne biyo bayan samun wasu bayanai na wasu mutane makusanta shugaban kasa da suke shirin tozarta shi a taron jam’iyyar da za a yi ranar Laraba.”

Sai dai majiyar ta musanta wani rahoto da ke cewa shugaba Tinubu ne ya bukaci Adamu ya yi murabus gabanin taron majalisar zartarwa na jam’iyyar na kasa da za a yi ranar Laraba. Jam’iyyar ta tsayar da ranakun 10 da 11 ga watan Yuli domin gudanar da tarukan kwamitinta na kasa da na NEC domin warware matsalolin da suka shafi rikicin kwamitin gudanarwar Jam’iyyar na kasa (NWC).

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Sai dai daga baya an dage tarukan da aka shirya zuwa ranar Larabar nan.

Wani mamba a jam’iyyar ya ce, Adamun ya yi murabus ne a lokacin da ya bayanan shirin wasu mutane biyu masu fada a ji a kusa da shugaban kasar na shirin kulla masa tuggun siyasa da tozarta shi.

“Ya yi murabus ne saboda sun fara sanya hannu don tsige shi a tarurrukan Jam’iyyar da za a gabatar. Ya yi murabus ne domin ya tseratar da kansa daga wulakanci,” cewar dan Jam’iyyar

Da aka tuntubi Adamu, ya shaida cewa ba zai ce uffan ba kan lamarin har sai Shugaba Tinubu ya dawo daga taron AU.

“Ba zan yi magana kan wannan batun ba saboda shugaban kasa ba ya nan,” in ji Adamu

Idan dai ba a manta ba, tun da jimawa gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC, Adamu ya ayyana tsohon shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a matsayin dan takarar jam’iyyar a shugabancin kasa.

Wannan furuci da Adamu ya yi ya haifar da hargitsi a cikin jam’iyyar a wancan lokacin, yayin da gwamnonin jam’iyyar daga Arewa suka rufar masa suna masu nuna goyan bayansu game Tinubu.

Matsayin gwamnonin ya tilastawa jam’iyyar bude koffar neman tikitin takarar shugaban kasa ga kowa, inda Tinubu ya lashe zaben.

Ko a kwanakin nan an jiyo, Adamu na sukar jerin sunayen shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da kakakin majalisar, Tajudeen Abbas, kan sunayen da suka bayyana a matsayin shugabancin majalisun biyu.

Bayan faruwar lamarin, shugaba Tinubu ya gayyaci Adamu zuwa fadar fadar shugaban kasa, inda aka warware matsalolin a yayin zaman.

Abdullahi
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Shehun Borno Ya Bukaci Jama’ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

Shehun Borno Ya Bukaci Jama'ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.