ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abdullahi Adamu Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Jam’iyyar APC Na Kasa

by Muhammad
3 years ago
Abdullahi

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu, ya mika takardar ajiye mukaminsa a daren ranar Lahadi, kamar yadda rahotanni suka tabbatar da hakan.

Wata majiya ta tabbatar wa da cewa Adamu, wanda ya zama shugaban jam’iyyar na kasa a babban taron jam’iyyar na kasa da aka gudanar cikin watan Maris din shekarar 2022, ya aike da takardar murabus dinsa zuwa fadar shugaban kasa ta da ke Abuja gabanin dawowar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu daga taron kungiyar tarayyar Afrika (AU) a kasar Kenya.

  • Rikicin APC: Kujerar Abdullahi Adamu Tana-kasa-tana-dabo
  • Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Daya daga cikin majiyar ta ce Adamu, tsohon gwamnan jihar Nasarawa, ya aika wasikar murabus din ga shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila, da misalin karfe 4 na yammacin ranar Lahadi.

ADVERTISEMENT

Kazalika, wata majiya daga bangaren Adamu ta tabbatar da hakan, inda ta kara da cewa, “Shugaban Jam’iyyar APC na kasa ya yi murabus ne biyo bayan samun wasu bayanai na wasu mutane makusanta shugaban kasa da suke shirin tozarta shi a taron jam’iyyar da za a yi ranar Laraba.”

Sai dai majiyar ta musanta wani rahoto da ke cewa shugaba Tinubu ne ya bukaci Adamu ya yi murabus gabanin taron majalisar zartarwa na jam’iyyar na kasa da za a yi ranar Laraba. Jam’iyyar ta tsayar da ranakun 10 da 11 ga watan Yuli domin gudanar da tarukan kwamitinta na kasa da na NEC domin warware matsalolin da suka shafi rikicin kwamitin gudanarwar Jam’iyyar na kasa (NWC).

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Sai dai daga baya an dage tarukan da aka shirya zuwa ranar Larabar nan.

Wani mamba a jam’iyyar ya ce, Adamun ya yi murabus ne a lokacin da ya bayanan shirin wasu mutane biyu masu fada a ji a kusa da shugaban kasar na shirin kulla masa tuggun siyasa da tozarta shi.

“Ya yi murabus ne saboda sun fara sanya hannu don tsige shi a tarurrukan Jam’iyyar da za a gabatar. Ya yi murabus ne domin ya tseratar da kansa daga wulakanci,” cewar dan Jam’iyyar

Da aka tuntubi Adamu, ya shaida cewa ba zai ce uffan ba kan lamarin har sai Shugaba Tinubu ya dawo daga taron AU.

“Ba zan yi magana kan wannan batun ba saboda shugaban kasa ba ya nan,” in ji Adamu

Idan dai ba a manta ba, tun da jimawa gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar APC, Adamu ya ayyana tsohon shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, a matsayin dan takarar jam’iyyar a shugabancin kasa.

Wannan furuci da Adamu ya yi ya haifar da hargitsi a cikin jam’iyyar a wancan lokacin, yayin da gwamnonin jam’iyyar daga Arewa suka rufar masa suna masu nuna goyan bayansu game Tinubu.

Matsayin gwamnonin ya tilastawa jam’iyyar bude koffar neman tikitin takarar shugaban kasa ga kowa, inda Tinubu ya lashe zaben.

Ko a kwanakin nan an jiyo, Adamu na sukar jerin sunayen shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da kakakin majalisar, Tajudeen Abbas, kan sunayen da suka bayyana a matsayin shugabancin majalisun biyu.

Bayan faruwar lamarin, shugaba Tinubu ya gayyaci Adamu zuwa fadar fadar shugaban kasa, inda aka warware matsalolin a yayin zaman.

Abdullahi
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Shehun Borno Ya Bukaci Jama’ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

Shehun Borno Ya Bukaci Jama'ar Jihar Borno Da Su Fito Rokon Ruwa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.