• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Barkewar Cutar Diptheria A Abuja

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Diptheria

An samu barkewar cutar Diphtheria da ta kashe yaro mai shekara hudu a garin Dei-Dei da ke babban birnin tarayya Abuja, wanda hakan ya sa hankalin mutane ya tashi musamman ma la’akari da yadda kwayar cutar take yaduwa tsakanin mutane.

Hukumar Babban Birnin Tarayya ta tabbatar da yaduwar cutar bayan da aka yi gwajin mutane takwas a dakin gwajin da ke Gaduwa da hukumar hana yaduwar cutar ta gudanar.

  • Bukatar Dakatar Da Kara Kudin Wutar Lantarki A Nijeriya
  • Kamfanin Meta Mamallakin Facebook Ya Yi Wa Twitter Kishiya

Diphtheria cuta ce da take farawa da zazzabi wanda yake saurin yaduwa ta hanyar tari da kuma hamma, kamar yadda hukumar lafiya ta duniya ta tabbatar.

 “Idan abin ya ta’azzara, kwayar cutar tana iya yin guba da take sa wani farin abu a bayan makogwaro wanda ke toshe hanyoyin da iska za ta shiga, abin da zai samar da matsala wajen shakar iska ko hadiya, da haka ne sai a fara tari mai zafi. Akwai wani sashe na wuya na iya kumburi saboda kwayar cutar ta yi sanadiyar ta kama wurin.

 “A hankali gubar na iya haduwa da jini wanda hakan na iya samar da matsala da lalata naman zuciya da za su iya shafar jijiya, koda da saboda karancin kwayar halitta ta jini da ke sa rauni saurin warkewa”.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

Cutar ana yin maganinta ta hanyar amfani da magani da kuma na yin allurar Diphtheria.

Domin kauce wa kamuwa da cutar, babban sakataren kula da lafiya na Abuja, Yahaya Batsa, ya yi kira da mutane su je su yi allurar rigakafi, su yi nesa da shiga cikin jama’a da kuma daina zama wuraren da babu tsafta. Ya ba da shawarar a yi wa yara allurar rigakafi kamar yadda ya dace sau uku na allurar Pentabalent.

Hukumar lafiya ta duniya ta yi bayanin cewar a tabbatar da yin allurar rigakafin cutar Diphtheria ga yara da samari, saboda gujewar barkewar cutar.

Akwai allurar rigakafi ta da take bukatar ba kamar yadda ake yi ba sau uku, wanda hakan zai sa a samu damar yi wa yara da yawa allurar rigakafin da ya kamata saboda kariya daga kamuwa da cututtuka kamar su Diphtheria.

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya yana sa ran hukumar lafiya ta duniya za ta assasa yin allurar rigakafi nan da wata uku masu zuwa ko rubi’in shekarar 2023.

Alkalumma da aka samu daga hukumar lafiya ta duniya sun nuna cewa an samu wadanda suka kamu da cutar Diptheria 557 a Nijeriya daga watan Afrilu na 2023, ya shafi jihohi 21 daga cikin 36 tare da babban birnin tarayya.

An sanar da cibiyar hana yaduwar cututtuka da maganisu ta kasa a watan Disamba 2022, dangane da barkewar cutar Diphtheria a jihohin Kano da Legas.

Daga ranar 14 ga watan Mayu zuwa 9 ga Afrilu 2022, an samu wadanda ake kyautata sun kamu da cutar guda 1439, amma daga karshe an samu 557 ko kashi 39 da aka tabbatar da sun kamu da mutuwar mutum 73 daga cikin wadanda suka kamu da cutar.

A Nijeriya an fara samun labarin barkewar cutar Diphtheria a shekarar 2011 da ta shafi wasu wurare a kauyukan Jihar Borno, sashen Arewa maso gabas.

Alamun kamuwa da cutar sun hada da zazzabi, majina ta rika zuba, ciwon mashako, tari, idanu su yi ja, kumburin wuya, sai samun matsalar yin numfashi. Cutar Diphtheria tana saurin yaduwa ta hanyar cudanya da wanda ya kamu da ita.

Domin tabbatar da an kauce wa yiyuwar kamuwa da cutar, an yi kira da mazauna babban burnin tarayya su tabbatar da an yi wa ‘ya’yansu alluran rigakafi sau uku na Pentabalent wato yadda aka amince da sharuddan alluran rigakafi na kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
Labarai

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Next Post
An Bude Dandalin Hadin Gwiwa Da Raya Kirkire-kirkire Na Sin Da Afirka

An Bude Dandalin Hadin Gwiwa Da Raya Kirkire-kirkire Na Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.