ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Dakatar Da Kara Kudin Wutar Lantarki A Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
Lantarki

Hankoron Nijeriya na shiga sahun kasashe masu bunkasar tattalin arzki da masana’antu ya rushe a ‘yan shekarun nan ne saboda rashin tsayayyar wutar lantarki a sassan kasa.

Ga kasar da ke da al’umma fiye da mutum miliyan 200 a yanzu ana iya samar da karfin wutan lantarki ne da ya kai megawatt 13,000 kacal, amma kuma megawatt 4,000 ne kawai ake iya rarraba wa al’umma saboda matsalolin da suka shafi rashin ingantattun na’u’rorin rarraba wutar lantarkin. Ba abin mamaki ba ne yadda ake samun yawaitar rashin wuta da lalacewar na’urorin rarraba wutar, abin da kuma yake haifar da koma baya ga zamantakewa da harkokin kasuwanci a sassan Nijeriya.

  • Amsar Xi Jinping Ta Ba Duniya Damar Fahimtar Tsarin Binciken Hada-hadar Kudin Na Kasar Sin
  • Gwamnan Zamfara Ya Rage Yawan Adadin Ma’aikatun Jihar Daga 28 Zuwa 16

Watakila saboda ganin muhimmancin wutar lantarki ga harkokin raya kasa ya sanya Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu a kan dokar gyara da kwaskwarima ga bangaren wutar lantarkin Nijeriya a cikin kwanaki 10 da hawansa karagar mulkin, ya sanya hannu a kan dokar wutar lantarki ta shekara 2023 inda aka maye gurbinta da dokar ta shekara 2005, inda aka sake fasalin dokar don ta yi daidai da wannan zamanin da ake ciki.

ADVERTISEMENT

Dokar za ta samar da yanayin da zai karfafa masu zuba jari a bangaren wutar lantarki musamman a kan abin da ya shafi rarraba wutar lantarki, ta yadda kamfanoni masu zaman kansu za su shigo don aiwatar da tadane-tanaden dokar don amfanin al’ummar kasa da bunkasar tattalin arziki Nijeriya.

A cikin sabuwar dokar, an sahallewa jihohi su bayar da lasisi ga masu zuba jari don su samar da kananan tashoshin samar da wutar lantarki a cikin jihohinsu amma dokar ta haramta rarraba wuta a tsakanin jihohi, ba kamar yadda abin yake a can baya ba.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A karkashin sabuwar dokar ta shekarar 2023, Hukumar Rarraba Wutar Lantarki (NERC) za ta samu damar sanya ido a kan harkokin rarraba wutar lantarki a Nijeriya ba tare da ta yi katsalandan da dokar da da ta ba jihohi ikon gudanar da nasu harkokin ba, amma kuma doka ta bata hurumin sa ido a kan yadda al’amurra ke tafiya a jihohin gaba daya.

Dokar ta kuma bayyana yadda hukumar NERC za ta mika harkokin gudanarwa ga kamfanonin da aka kafa na wutar lantarki a jihohi ba tare da an samu wata matsala ba. Amma kuma NERC za ta ci gaba da sanya ido a kan yadda wadannan kamfanonin ke gudanar da aikinsu har sai jihohin sun kafa nasu dokokin da za su sa ido a kan harkokin kamfanonin da aka kafa. A halin yanzu jihohin Legas, Edo, da Kaduna ne kawai suka samar da dokokin sa ido a harkokin kasuwancin wutar lantarki a Nijeriya.

Wani sabon lamari a cikin sabuwar dokar ya hada da amincewar da aka yi mutum na iya samar wa kansa wutar lantarki don amfanin kansa amma wutar da bai wuce megawatt 1 (MW) ba, amma kuma hukumar NERC ke a ikon sanya ido a kan irin wannan shirin tare da sabunta da lasisi daga lokaci zuwa lokaci.

A mastayinmu na gidan jarida, muna masu yaba wa shugaban kasa a kan yadda ya sa hannu a kan sabuwar dokar, musamman ganin yadda masu ruwa da tsaki suka dade suna ta kiran a samar da yanayin da bangaren wutar lantarki zai yi bunkasar da ta dace, dokar ta fitar da dukkan matsalolin da ke haifar da cikas a kokarin bunkasar bangaren samar da wutar lantarki a Nijeriya, dokar kuma za ta karfafa tare da jawo masu zuba jari a ciki da wajen kasar nan wanda ba sai an fada ba hakan zai samar da bunkasar tattalin arziki saboda manya da kananan masa’nantun Nijeriya za su bunkasa, abin kuma da zai taimaka wajen samar da aikin yi ga dimbin matasan Nijeriya.

Karin jihohi da kanfanoni masu zaman kansu a bangaren samar da wutar lantarki zai karfafa bangaren wutar lantarki ta hanyar samar da sabbin kayan aiki da kwararru daga kasashen waje wadanda za su bayar da gudummawarsu da sabuwar fasahar samar da rarraba wuta lantarkin.

In har aka samu karin jihohi da sabbin kamfanoni a bangaren kamar an yi maganin abin da ya shafi yadda ake samun matsala wajen karbar kudaden wuta ne daga hannun al’umma, hakan zai kai ga samun karin kudaden shiga ga jihohi wanda zai kuma kai ga aiwatar da ayyukan raya kasa da karin zuba jari.

Sau da dama a Nijeriya babbar matsalar da aka fi fuskanta ita ce na aiwatar da tsare-tsare da wai kafa doka ba, a kan haka muke kira da a tabbatar an aiwatar da dokar yadda ya kamata.

Karin kudin wuta da aka yi a kwanan nan da kashi 40 abu ne da ya tayar da hankulan al’ummar Nijeriya, wannan na zuwa ne a yayin da ake fuskantar hauhawar farashin kayan masarufi, tabbas ya kamata a duba wannan karin da aka yi da nufin samar da yanayin da za a rage wa al’umma matsalolin da suke ciki.

Tuni kungiyar kwadago ta NLC ta nemi a gaggauta dakatar da karin kudin wutar lantarkin sai zuwa wani lokaci da al’murra suka daidaita, wannan na da matukar muhimmanci kuma ya kamata gwamnati ta sanya baki don ganin a samar da daidaito a kudin da za a kara don tabbas al’umma da fama matsalar rayuwa.

Lantarki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Tirka-tirkar Daliba Ejikeme Mmesoma: Masani Ya Tona Asirin Yadda Ake Sauya Sakamakon JAMB Na Bogi

Tirka-tirkar Daliba Ejikeme Mmesoma: Masani Ya Tona Asirin Yadda Ake Sauya Sakamakon JAMB Na Bogi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.