• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Farashin Amfanin Gona Ke Ci Gaba Da Tashi A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gona

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Farashin kayan abinci a Nijeriya na ci gaba da tashin gwauron zabi; wanda za a iya cewa, ba a taba ganin irin hakan a shekaru da dama da suka wuce a wannan kasar ba.

Wannan matsalar na faruwa ce a yayin da wasu manona har yanzu ke kan yin girbin amfanin gonakinsu. Babu shakka, hakan na ci gaba da jefa fargaba a zukatan masu ruwa da tsaki a kan yadda matsalar za ta yi wa  fannin tattalin arzikin kasa illa tare da jawo rashin samar da  wadatacen abinci a wannan kasa.

  • Rikicin Siyasar Jihar Ribas:  Dattawa Da Kabilar Ijaw Sun Yi Fatali Da Sabon Sulhu Bisa Zargin Kashin Dankali
  • Kamfanin Man Nijeriya Ya Sa Hannu Kan Fasahar Gano Sinadarin Methane

Sai dai, ba Nijeriya ce kadai ke fuskantar irin wannan kalubale ba, musamman ganin cewa kasar ta mayar da hankali ne wajen shigo da amfanin gona daga kasashen ketare kamar abin da ya shafi Rogo da Doya da sauran kayan abinci.

Kazalika, Nijeriya na fuskantar karancin abinci kamar Masara, Alkama da Waken Soya. Har ila yau, faduwar darajar naira a kasar ya kara tabarbara al’amura wajen shigo da kayan abinci cikin kasar.

Abin Da Ya Sa Farashin Abinci ke Tashi:

Wani bincike da aka gudanar a wasu manyan kasuwannin kasar nan da ake yin hada-hadar sayar da hatsi ya nuna cewa, duk da manoma sun girbe amfani mai yawa a noman da aka yi na bana, amma farashin kayan abinici na ci gaba da tashin gwauran zabi.

Misali a Jihar Katsina, farashin na ci ngaba da tashi; inda lamarin ke ci gaba da tayar wa da magidanta hankali, musamman ganin cewa, ana fara shirin shiga sabuwar shekarar 2024 ta fara yin wani noman.

Wani dilan sayar da hatsi a Jihar Kano, Alhaji Sa’adu Abashe ya yi nuni da cewa, akasarin mutane ba su da masaniya a kan abin da ke jawo tashin farashin amfanin gonar da aka noma na bana.

Sannan, ya danganta tashin farashin a kan faduwar darajar naira da tsadar takin zamani da kayan aikin noma da kudaden da ake biyan ‘yan kwadago da tsadar farashin man fetur da kuma kudin da manoma ke kashe wa domin yin jigilar amfanin da suka noma daga gonakinsu zuwa kasuwanni don sayarwa.

Sa’adu ya kara da cewa, farashin Masara, Dawa, Waken Soya, Gero da kuma Shinkafa ya yi matukar karuwa, inda kowane buhu daya mai nauyin kilo 100 ya kai kimanin naira 30,000.

Shi kuwa wani babban dan kasuwa a kasuwar Dandume da ke a Jihar Katsina, Alhaji Muhammad Salisu ya sanar da cewa, gannin yadda a bara masu sayen hatsi suna boyewa, don sayar da shi da tsada sun samu makudan kudade, hakan ne ya sa wasu masu kudin su ma suka sayi amfanin gonar da dama da aka noma a bana; suka boye domin  samun kazamar riba.

Ya ce, wadanda suka sayi duk buhun Masara daya a kan naira 18,000 zuwa Naira 22,000, yanzu suna sayar da duk buhu guda kan akalla naira 55,000.

Shi kuwa Shugaban Kaungiyar Manoma Reshen Jihar Kano (AFAN), Malam Abdulrasheed Magaji Rimingado, ya danganta tashin farashin ne kan yadda wasu kamfanoni da ke sarrafa amfanin gonar zuwa wasu nau’ikan abinci ke yin rige-rigen saye amfanin da kuma tsadar jigilar amfanin gona.

A Jihar Neja kuwa, ‘yan kasuwa da manoma a jihar sun dangata tashin farashin a kan yadda ake yawan bukatar amfanin gonar. Shugaban masu sayar da hatsi a kasuwar sayar da hatsi ta Lemu a Karamar Hukumar Gbako, Alhaji Danladi Kowangi cewa ya yi; farashin buhun Shinkafar da ake nomawa a kasar nan ya tashi daga naira 22,000 zuwa naira 26,000, duk kuwa da cewa manoman sun jima da girbe Shinkafar.

Kowangi ya kara da cewa, sannan duk buhun Masara guda a halin yanzu, ana sayar da shi a kan naira 35,000, inda kuma ake sayar da buhun Gero a kan naira 35,000 a wannan kasuwa ta Lemu.

Har ila yau, a kasuwar Batati da ke Karamar Hukumar Labun a jihar da ake samun kayan abinci a cikin rahusa, ana sayar da duk buhun Dawa a kan naira 30,000, Gero naira 23,000, sai buhun jan Wake kuma a kan naira 40,000 zuwa naira 45,000.

A Karamar Hukumar Saminaka da ke Jihar Kaduna kuwa, shugaban masu sayar da hatsi a kasuwar, Manu Isah Idris ya danganta abubuwa da dama da suka jawo ci gaba da tashin farashin a daidai wannan lokaci; daga cikinsu a cewar tasa akwai batun yakin da ake ci gaba da yi a Kasashen Ukraine da kuma Kasar Falasdin tare kuma da cire tallafin man fetur wanda gwamnatin tarayya ta yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.