• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Farashin Amfanin Gona Ke Ci Gaba Da Tashi A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abin Da Ya Sa Farashin Amfanin Gona Ke Ci Gaba Da Tashi A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Farashin kayan abinci a Nijeriya na ci gaba da tashin gwauron zabi; wanda za a iya cewa, ba a taba ganin irin hakan a shekaru da dama da suka wuce a wannan kasar ba.

Wannan matsalar na faruwa ce a yayin da wasu manona har yanzu ke kan yin girbin amfanin gonakinsu. Babu shakka, hakan na ci gaba da jefa fargaba a zukatan masu ruwa da tsaki a kan yadda matsalar za ta yi wa  fannin tattalin arzikin kasa illa tare da jawo rashin samar da  wadatacen abinci a wannan kasa.

  • Rikicin Siyasar Jihar Ribas:  Dattawa Da Kabilar Ijaw Sun Yi Fatali Da Sabon Sulhu Bisa Zargin Kashin Dankali
  • Kamfanin Man Nijeriya Ya Sa Hannu Kan Fasahar Gano Sinadarin Methane

Sai dai, ba Nijeriya ce kadai ke fuskantar irin wannan kalubale ba, musamman ganin cewa kasar ta mayar da hankali ne wajen shigo da amfanin gona daga kasashen ketare kamar abin da ya shafi Rogo da Doya da sauran kayan abinci.

Kazalika, Nijeriya na fuskantar karancin abinci kamar Masara, Alkama da Waken Soya. Har ila yau, faduwar darajar naira a kasar ya kara tabarbara al’amura wajen shigo da kayan abinci cikin kasar.

Abin Da Ya Sa Farashin Abinci ke Tashi:

Wani bincike da aka gudanar a wasu manyan kasuwannin kasar nan da ake yin hada-hadar sayar da hatsi ya nuna cewa, duk da manoma sun girbe amfani mai yawa a noman da aka yi na bana, amma farashin kayan abinici na ci gaba da tashin gwauran zabi.

Misali a Jihar Katsina, farashin na ci ngaba da tashi; inda lamarin ke ci gaba da tayar wa da magidanta hankali, musamman ganin cewa, ana fara shirin shiga sabuwar shekarar 2024 ta fara yin wani noman.

Wani dilan sayar da hatsi a Jihar Kano, Alhaji Sa’adu Abashe ya yi nuni da cewa, akasarin mutane ba su da masaniya a kan abin da ke jawo tashin farashin amfanin gonar da aka noma na bana.

Sannan, ya danganta tashin farashin a kan faduwar darajar naira da tsadar takin zamani da kayan aikin noma da kudaden da ake biyan ‘yan kwadago da tsadar farashin man fetur da kuma kudin da manoma ke kashe wa domin yin jigilar amfanin da suka noma daga gonakinsu zuwa kasuwanni don sayarwa.

Sa’adu ya kara da cewa, farashin Masara, Dawa, Waken Soya, Gero da kuma Shinkafa ya yi matukar karuwa, inda kowane buhu daya mai nauyin kilo 100 ya kai kimanin naira 30,000.

Shi kuwa wani babban dan kasuwa a kasuwar Dandume da ke a Jihar Katsina, Alhaji Muhammad Salisu ya sanar da cewa, gannin yadda a bara masu sayen hatsi suna boyewa, don sayar da shi da tsada sun samu makudan kudade, hakan ne ya sa wasu masu kudin su ma suka sayi amfanin gonar da dama da aka noma a bana; suka boye domin  samun kazamar riba.

Ya ce, wadanda suka sayi duk buhun Masara daya a kan naira 18,000 zuwa Naira 22,000, yanzu suna sayar da duk buhu guda kan akalla naira 55,000.

Shi kuwa Shugaban Kaungiyar Manoma Reshen Jihar Kano (AFAN), Malam Abdulrasheed Magaji Rimingado, ya danganta tashin farashin ne kan yadda wasu kamfanoni da ke sarrafa amfanin gonar zuwa wasu nau’ikan abinci ke yin rige-rigen saye amfanin da kuma tsadar jigilar amfanin gona.

A Jihar Neja kuwa, ‘yan kasuwa da manoma a jihar sun dangata tashin farashin a kan yadda ake yawan bukatar amfanin gonar. Shugaban masu sayar da hatsi a kasuwar sayar da hatsi ta Lemu a Karamar Hukumar Gbako, Alhaji Danladi Kowangi cewa ya yi; farashin buhun Shinkafar da ake nomawa a kasar nan ya tashi daga naira 22,000 zuwa naira 26,000, duk kuwa da cewa manoman sun jima da girbe Shinkafar.

Kowangi ya kara da cewa, sannan duk buhun Masara guda a halin yanzu, ana sayar da shi a kan naira 35,000, inda kuma ake sayar da buhun Gero a kan naira 35,000 a wannan kasuwa ta Lemu.

Har ila yau, a kasuwar Batati da ke Karamar Hukumar Labun a jihar da ake samun kayan abinci a cikin rahusa, ana sayar da duk buhun Dawa a kan naira 30,000, Gero naira 23,000, sai buhun jan Wake kuma a kan naira 40,000 zuwa naira 45,000.

A Karamar Hukumar Saminaka da ke Jihar Kaduna kuwa, shugaban masu sayar da hatsi a kasuwar, Manu Isah Idris ya danganta abubuwa da dama da suka jawo ci gaba da tashin farashin a daidai wannan lokaci; daga cikinsu a cewar tasa akwai batun yakin da ake ci gaba da yi a Kasashen Ukraine da kuma Kasar Falasdin tare kuma da cire tallafin man fetur wanda gwamnatin tarayya ta yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Abubuwa 5 Da Ke Kawo Nakasu Wajen Koyon Ilimi (2)

Next Post

An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 week ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

2 weeks ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Next Post
An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

July 1, 2025
Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

July 1, 2025
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

July 1, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

July 1, 2025
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.