• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Farashin Amfanin Gona Ke Ci Gaba Da Tashi A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abin Da Ya Sa Farashin Amfanin Gona Ke Ci Gaba Da Tashi A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

Farashin kayan abinci a Nijeriya na ci gaba da tashin gwauron zabi; wanda za a iya cewa, ba a taba ganin irin hakan a shekaru da dama da suka wuce a wannan kasar ba.

Wannan matsalar na faruwa ce a yayin da wasu manona har yanzu ke kan yin girbin amfanin gonakinsu. Babu shakka, hakan na ci gaba da jefa fargaba a zukatan masu ruwa da tsaki a kan yadda matsalar za ta yi wa  fannin tattalin arzikin kasa illa tare da jawo rashin samar da  wadatacen abinci a wannan kasa.

  • Rikicin Siyasar Jihar Ribas:  Dattawa Da Kabilar Ijaw Sun Yi Fatali Da Sabon Sulhu Bisa Zargin Kashin Dankali
  • Kamfanin Man Nijeriya Ya Sa Hannu Kan Fasahar Gano Sinadarin Methane

Sai dai, ba Nijeriya ce kadai ke fuskantar irin wannan kalubale ba, musamman ganin cewa kasar ta mayar da hankali ne wajen shigo da amfanin gona daga kasashen ketare kamar abin da ya shafi Rogo da Doya da sauran kayan abinci.

Kazalika, Nijeriya na fuskantar karancin abinci kamar Masara, Alkama da Waken Soya. Har ila yau, faduwar darajar naira a kasar ya kara tabarbara al’amura wajen shigo da kayan abinci cikin kasar.

Abin Da Ya Sa Farashin Abinci ke Tashi:

Wani bincike da aka gudanar a wasu manyan kasuwannin kasar nan da ake yin hada-hadar sayar da hatsi ya nuna cewa, duk da manoma sun girbe amfani mai yawa a noman da aka yi na bana, amma farashin kayan abinici na ci gaba da tashin gwauran zabi.

Misali a Jihar Katsina, farashin na ci ngaba da tashi; inda lamarin ke ci gaba da tayar wa da magidanta hankali, musamman ganin cewa, ana fara shirin shiga sabuwar shekarar 2024 ta fara yin wani noman.

Wani dilan sayar da hatsi a Jihar Kano, Alhaji Sa’adu Abashe ya yi nuni da cewa, akasarin mutane ba su da masaniya a kan abin da ke jawo tashin farashin amfanin gonar da aka noma na bana.

Sannan, ya danganta tashin farashin a kan faduwar darajar naira da tsadar takin zamani da kayan aikin noma da kudaden da ake biyan ‘yan kwadago da tsadar farashin man fetur da kuma kudin da manoma ke kashe wa domin yin jigilar amfanin da suka noma daga gonakinsu zuwa kasuwanni don sayarwa.

Sa’adu ya kara da cewa, farashin Masara, Dawa, Waken Soya, Gero da kuma Shinkafa ya yi matukar karuwa, inda kowane buhu daya mai nauyin kilo 100 ya kai kimanin naira 30,000.

Shi kuwa wani babban dan kasuwa a kasuwar Dandume da ke a Jihar Katsina, Alhaji Muhammad Salisu ya sanar da cewa, gannin yadda a bara masu sayen hatsi suna boyewa, don sayar da shi da tsada sun samu makudan kudade, hakan ne ya sa wasu masu kudin su ma suka sayi amfanin gonar da dama da aka noma a bana; suka boye domin  samun kazamar riba.

Ya ce, wadanda suka sayi duk buhun Masara daya a kan naira 18,000 zuwa Naira 22,000, yanzu suna sayar da duk buhu guda kan akalla naira 55,000.

Shi kuwa Shugaban Kaungiyar Manoma Reshen Jihar Kano (AFAN), Malam Abdulrasheed Magaji Rimingado, ya danganta tashin farashin ne kan yadda wasu kamfanoni da ke sarrafa amfanin gonar zuwa wasu nau’ikan abinci ke yin rige-rigen saye amfanin da kuma tsadar jigilar amfanin gona.

A Jihar Neja kuwa, ‘yan kasuwa da manoma a jihar sun dangata tashin farashin a kan yadda ake yawan bukatar amfanin gonar. Shugaban masu sayar da hatsi a kasuwar sayar da hatsi ta Lemu a Karamar Hukumar Gbako, Alhaji Danladi Kowangi cewa ya yi; farashin buhun Shinkafar da ake nomawa a kasar nan ya tashi daga naira 22,000 zuwa naira 26,000, duk kuwa da cewa manoman sun jima da girbe Shinkafar.

Kowangi ya kara da cewa, sannan duk buhun Masara guda a halin yanzu, ana sayar da shi a kan naira 35,000, inda kuma ake sayar da buhun Gero a kan naira 35,000 a wannan kasuwa ta Lemu.

Har ila yau, a kasuwar Batati da ke Karamar Hukumar Labun a jihar da ake samun kayan abinci a cikin rahusa, ana sayar da duk buhun Dawa a kan naira 30,000, Gero naira 23,000, sai buhun jan Wake kuma a kan naira 40,000 zuwa naira 45,000.

A Karamar Hukumar Saminaka da ke Jihar Kaduna kuwa, shugaban masu sayar da hatsi a kasuwar, Manu Isah Idris ya danganta abubuwa da dama da suka jawo ci gaba da tashin farashin a daidai wannan lokaci; daga cikinsu a cewar tasa akwai batun yakin da ake ci gaba da yi a Kasashen Ukraine da kuma Kasar Falasdin tare kuma da cire tallafin man fetur wanda gwamnatin tarayya ta yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Abubuwa 5 Da Ke Kawo Nakasu Wajen Koyon Ilimi (2)

Next Post

An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

7 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

7 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

An Fara Gina Cibiyar UHD Highland Ta CMG

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.