• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Masu Saye Da Sayar Da Amfanin Gona A Kaduna Suka Ragu

by Abubakar Abba, Sulaiman and Abubakar Sulaiman
10 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dawanau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu kananun masu sayar da kayan masarufi kamar Doya, Masara da sauran makamantansu a Jihar Kaduna sun bayyana cewa, ci gaba da samun karancin kudaden shiga a wurin abokan cinikayyarsu da kuma samun hauhawar farashin kaya a fadin wannan kasa, ya sa abokan cinikayya ba sa iya sayen kayan nasu.

 

A hirarsu da LEADERSHIP Hausa a Kaduna sun bayyana cewa, saboda karancin kudade a hannun jama’a, hakan ya sa suke tabka asara wajen rashin samun kudaden shiga.

  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Kolin CEO Na APEC
  • Yadda Gwamna Nasir Idris Ya Daura Damarar Bunkasa Ilimi A Jihar Kebbi

Daya daga cikinsu, Kabiru Sani da ke sana’ar sayar da Masara a Kasuwar Kawo da ke a jihar ya bayyana cewa, hakan na jawo musu matukar koma baya a sana’ar tasu.

 

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Shi ma, wani mai sayar da Garin Kwaki; Auwal Muhammad ya sanar da cewa, yawan abokan cinikayyar da yake samu a baya, sun ragu sosai.

 

Ya danganta hakan, a kan rashin samun wadatattun kudade a hannun jama’a, inda ya kara da cewa; ga dai amfanin gona da dama a kasuwar, amma muna fuskantar kalubalen samun abokan cinikayya na yau da kullum.

 

Ita kuwa, wata mai sana’ar sayar da Doya a kasuwar Bakin Dogo; Hadiza Lawal ta sanar da cewa, ci gaba da samun hauhawar farashin kaya a kasar nan, ya jawo wasu abokan cinikayyarsu ba sa iya sayen Doyar duk da cewa, tuni sabuwar Doyar da aka noma a kakar noma bana na da yawa, inda ta kara da cewa; duk da karya farashin Doyar, abokan cinikayyar ‘yan kalilan ne ke iya saya.

 

Shi ma, wani karamin dan kasuwa mai sana’ar sayar da Dawa, Abdulrahim Abdullahi ya sanar da cewa, abokan cinikayyarsu sun yi matukar ragu.

 

A cewar Abdullahi, jama’a a halin yanzu ba sa iya sayen kaya kamar a baya, inda ya ce; idan abokin ciniki na da burin sayen misali mudu biyar, yanzu bai fi ya sayi mudu biyu ko uku ba; saboda tashin farashin da Dawar ya yi.

 

Shi ma, Muhammad Giyade mai sana’ar sayar da buhunhunan Shinkafa ya ce, tsadar ta sa ba ya samun abokan ciniki da dama; sabanin yadda yake samu a baya.

 

A cewarsa, hakan ya jawo rashin samun riba mai yawa da kuma rashin sayar da kayan da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

Next Post

Nasarar Trump Na Iya Shafar Hauhawar Farashi A Nijeriya – Rahoto

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

7 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

7 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

Nasarar Trump Na Iya Shafar Hauhawar Farashi A Nijeriya – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.