• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Masu Saye Da Sayar Da Amfanin Gona A Kaduna Suka Ragu

by Abubakar Abba, Sulaiman and Abubakar Sulaiman
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dawanau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu kananun masu sayar da kayan masarufi kamar Doya, Masara da sauran makamantansu a Jihar Kaduna sun bayyana cewa, ci gaba da samun karancin kudaden shiga a wurin abokan cinikayyarsu da kuma samun hauhawar farashin kaya a fadin wannan kasa, ya sa abokan cinikayya ba sa iya sayen kayan nasu.

 

A hirarsu da LEADERSHIP Hausa a Kaduna sun bayyana cewa, saboda karancin kudade a hannun jama’a, hakan ya sa suke tabka asara wajen rashin samun kudaden shiga.

  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Kolin CEO Na APEC
  • Yadda Gwamna Nasir Idris Ya Daura Damarar Bunkasa Ilimi A Jihar Kebbi

Daya daga cikinsu, Kabiru Sani da ke sana’ar sayar da Masara a Kasuwar Kawo da ke a jihar ya bayyana cewa, hakan na jawo musu matukar koma baya a sana’ar tasu.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Shi ma, wani mai sayar da Garin Kwaki; Auwal Muhammad ya sanar da cewa, yawan abokan cinikayyar da yake samu a baya, sun ragu sosai.

 

Ya danganta hakan, a kan rashin samun wadatattun kudade a hannun jama’a, inda ya kara da cewa; ga dai amfanin gona da dama a kasuwar, amma muna fuskantar kalubalen samun abokan cinikayya na yau da kullum.

 

Ita kuwa, wata mai sana’ar sayar da Doya a kasuwar Bakin Dogo; Hadiza Lawal ta sanar da cewa, ci gaba da samun hauhawar farashin kaya a kasar nan, ya jawo wasu abokan cinikayyarsu ba sa iya sayen Doyar duk da cewa, tuni sabuwar Doyar da aka noma a kakar noma bana na da yawa, inda ta kara da cewa; duk da karya farashin Doyar, abokan cinikayyar ‘yan kalilan ne ke iya saya.

 

Shi ma, wani karamin dan kasuwa mai sana’ar sayar da Dawa, Abdulrahim Abdullahi ya sanar da cewa, abokan cinikayyarsu sun yi matukar ragu.

 

A cewar Abdullahi, jama’a a halin yanzu ba sa iya sayen kaya kamar a baya, inda ya ce; idan abokin ciniki na da burin sayen misali mudu biyar, yanzu bai fi ya sayi mudu biyu ko uku ba; saboda tashin farashin da Dawar ya yi.

 

Shi ma, Muhammad Giyade mai sana’ar sayar da buhunhunan Shinkafa ya ce, tsadar ta sa ba ya samun abokan ciniki da dama; sabanin yadda yake samu a baya.

 

A cewarsa, hakan ya jawo rashin samun riba mai yawa da kuma rashin sayar da kayan da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

Next Post

Nasarar Trump Na Iya Shafar Hauhawar Farashi A Nijeriya – Rahoto

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

6 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

13 hours ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

Nasarar Trump Na Iya Shafar Hauhawar Farashi A Nijeriya – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.