• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Masu Saye Da Sayar Da Amfanin Gona A Kaduna Suka Ragu

by Abubakar Abba, Sulaiman and Abubakar Sulaiman
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dawanau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu kananun masu sayar da kayan masarufi kamar Doya, Masara da sauran makamantansu a Jihar Kaduna sun bayyana cewa, ci gaba da samun karancin kudaden shiga a wurin abokan cinikayyarsu da kuma samun hauhawar farashin kaya a fadin wannan kasa, ya sa abokan cinikayya ba sa iya sayen kayan nasu.

 

A hirarsu da LEADERSHIP Hausa a Kaduna sun bayyana cewa, saboda karancin kudade a hannun jama’a, hakan ya sa suke tabka asara wajen rashin samun kudaden shiga.

  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Kolin CEO Na APEC
  • Yadda Gwamna Nasir Idris Ya Daura Damarar Bunkasa Ilimi A Jihar Kebbi

Daya daga cikinsu, Kabiru Sani da ke sana’ar sayar da Masara a Kasuwar Kawo da ke a jihar ya bayyana cewa, hakan na jawo musu matukar koma baya a sana’ar tasu.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Shi ma, wani mai sayar da Garin Kwaki; Auwal Muhammad ya sanar da cewa, yawan abokan cinikayyar da yake samu a baya, sun ragu sosai.

 

Ya danganta hakan, a kan rashin samun wadatattun kudade a hannun jama’a, inda ya kara da cewa; ga dai amfanin gona da dama a kasuwar, amma muna fuskantar kalubalen samun abokan cinikayya na yau da kullum.

 

Ita kuwa, wata mai sana’ar sayar da Doya a kasuwar Bakin Dogo; Hadiza Lawal ta sanar da cewa, ci gaba da samun hauhawar farashin kaya a kasar nan, ya jawo wasu abokan cinikayyarsu ba sa iya sayen Doyar duk da cewa, tuni sabuwar Doyar da aka noma a kakar noma bana na da yawa, inda ta kara da cewa; duk da karya farashin Doyar, abokan cinikayyar ‘yan kalilan ne ke iya saya.

 

Shi ma, wani karamin dan kasuwa mai sana’ar sayar da Dawa, Abdulrahim Abdullahi ya sanar da cewa, abokan cinikayyarsu sun yi matukar ragu.

 

A cewar Abdullahi, jama’a a halin yanzu ba sa iya sayen kaya kamar a baya, inda ya ce; idan abokin ciniki na da burin sayen misali mudu biyar, yanzu bai fi ya sayi mudu biyu ko uku ba; saboda tashin farashin da Dawar ya yi.

 

Shi ma, Muhammad Giyade mai sana’ar sayar da buhunhunan Shinkafa ya ce, tsadar ta sa ba ya samun abokan ciniki da dama; sabanin yadda yake samu a baya.

 

A cewarsa, hakan ya jawo rashin samun riba mai yawa da kuma rashin sayar da kayan da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Masu Kiwon ‘Yan Tsakin Gidan Gona Ke Ganin Tasku A Kano

Next Post

Nasarar Trump Na Iya Shafar Hauhawar Farashi A Nijeriya – Rahoto

Related

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

5 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

6 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

6 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

7 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Next Post
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

Nasarar Trump Na Iya Shafar Hauhawar Farashi A Nijeriya – Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.